< 2 Královská 11 >

1 Atalia pak matka Ochoziášova viduci, že umřel syn její, vstavši, pomordovala všecko símě královské.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 Ale Jozaba dcera krále Jehorama, sestra Ochoziášova, vzala Joasa syna Ochoziášova, a ukradši ho z prostředku synů královských, kteříž mordováni byli, skryla jej i s chůvou jeho v pokoji, kdež lůže byla. A tak skryli ho před Atalií, a není zamordován.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 I byl s ní v domě Hospodinově tajně za šest let, v nichž Atalia kralovala nad zemí.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 Léta sedmého poslav Joiada, povolal setníků, hejtmanů a drabantů. I uvedl je k sobě do domu Hospodinova, a učinil s nimi smlouvu, a zavázav je přísahou v domě Hospodinově, ukázal jim syna králova.
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 A přikázal jim, řka: Tato jest věc, kterouž učiníte: Třetí díl vás, kteříž přicházíte v sobotu, a držíte stráž, bude při domě králově,
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 A díl třetí bude u brány Sur, a třetí díl bude u brány za drabanty, a budete stráž držeti, ostříhajíce domu tohoto před outokem.
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 Vy pak všickni, kteříž byste odjíti měli v sobotu, po vykonání povinnosti při domě Hospodinově, ve dvě poboční stráže rozdělení, buďte při králi.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 A tak obstoupíte krále vůkol, jeden každý majíce braň svou v rukou svých. Kdož by pak šel do šiku vašeho, ať umře; a budete při králi, když bude vycházeti i když bude vcházeti.
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 Protož učinili setníci ti všecky věci tak, jakž byl rozkázal Joiada kněz, a vzavše jeden každý muže své, kteříž přicházeli v sobotu a kteříž odcházeli v sobotu, přišli k Joiadovi knězi.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 I dal kněz setníkům kopí a pavézy, kteréž byly Davida krále, a kteréž byly v domě Hospodinově.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 Stáli pak ti drabanti, jeden každý držíce braň svou v ruce své, od pravé strany domu až do levé strany domu, proti oltáři a proti domu při králi vůkol.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 Tedy vyvedl syna králova, a vstavil na něj korunu a ozdobu. I ustanovili jej králem a pomazali ho, a plésajíce rukama, říkali: Živ buď král!
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 V tom uslyševši Atalia hluk plésajícího lidu, vešla k lidu do domu Hospodinova.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 A když pohleděla, a aj, král stál na místě vyšším, vedlé obyčeje s knížaty, a trouby byly před králem, a všecken lid země byl vesel, i troubili v trouby. Tedy roztrhla Atalia roucho své a zkřikla: Spiknutí, spiknutí!
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 Protož rozkázal Joiada kněz těm setníkům ustaveným nad vojskem, řka jim: Pusťte ji prostředkem řadu, a i toho, kdož by za ní šel, zabíte mečem. Nebo byl řekl kněz: Ať není zabita v domě Hospodinově.
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 I pustili ji. Ale když přišla na cestu, kudy koni vcházejí do domu královského, tu jest zabita.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Tedy učinil Joiada smlouvu mezi Hospodinem a mezi králem, i mezi lidem, aby byli lid Hospodinův; též mezi králem a mezi lidem.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 Potom šel všecken lid země do domu Bálova, a zbořili jej, i oltáře jeho a obrazy jeho v kusy stroskotali; Matana také kněze Bálova zabili před oltáři. Kněz pak znovu nařídil přisluhující v domě Hospodinově.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 A pojav ty setníky a hejtmany, i drabanty se vším lidem země, provázeli krále z domu Hospodinova, a přišli cestou k bráně drabantů do domu královského. Kdežto posadil se na stolici královské.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 I veselil se všecken lid země, a město se upokojilo. Atalii pak zabili mečem u domu královského.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 A byl Joas v sedmi letech, když počal kralovati.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Královská 11 >