< 2 Kronická 27 >

1 V pětmecítma letech byl Jotam, když počal kralovati, a šestnáct let kraloval v Jeruzalémě. Jméno matky jeho Jerusa dcera Sádochova.
Yotam yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida. Sunan mahaifiyarsa Yerusha,’yar Zadok.
2 Kterýž činil to, což pravého bylo před očima Hospodinovýma, podlé všeho, což činil Uziáš otec jeho, kromě že nevšel do chrámu Hospodinova, a lid ještě porušený byl.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar yadda mahaifinsa Uzziya ya yi, sai dai bai kutsa cikin haikalin Ubangiji kamar mahaifinsa ba. Mutane kuwa, suka ci gaba da aikata ayyukan lalaci.
3 On ustavěl bránu domu Hospodinova hořejší, a na zdi Ofel mnoho stavěl.
Yotam ya sāke ginin Ƙofar Bisa na haikalin Ubangiji, ya kuma yi aiki sosai a katanga a tudun Ofel.
4 Nadto vystavěl i města na horách Judských, a v lesích zdělal zámky a věže.
Ya gina garuruwa a tuddan Yahuda, ya giggina katanga da gine-gine masu tsawo a wuraren da suke a kurmi.
5 On také bojoval s králem synů Ammon, a zmocnil se jich. I dali mu synové Ammon toho roku sto centnéřů stříbra, a deset tisíc měr pšenice, a ječmene deset tisíců. Tolikéž dali mu synové Ammon i léta druhého i třetího.
Yotam ya yi yaƙi da sarkin Ammonawa ya kuma ci su. A wannan shekara Ammonawa suka biya shi haraji talenti ɗari na azurfa, garwan alkama dubu goma da kuma garwa dubu goma na sha’ir. Ammonawa suka kawo masa wannan kuma a shekara ta biyu da ta uku.
6 A tak zsilil se Jotam; nebo nastrojil cesty své před Hospodinem Bohem svým.
Yotam ya ƙaru a iko saboda ya daidaita al’amuransa a gaban Ubangiji Allahnsa.
7 O jiných pak věcech Jotamových, a o všech válkách i cestách jeho, zapsáno jest v knize o králích Izraelských a Judských.
Sauran ayyuka a mulkin Yotam, haɗe da dukan yaƙe-yaƙensa da waɗansu abubuwan da ya yi, suna a rubuce a littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
8 V pětmecítma letech byl, když kralovati začal, a šestnáct let kraloval v Jeruzalémě.
Yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha shida.
9 I usnul Jotam s otci svými, a pochovali jej v městě Davidově, a kraloval Achas syn jeho místo něho.
Yotam ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a Birnin Dawuda. Sai Ahaz ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.

< 2 Kronická 27 >