< 2 Kronická 19 >

1 Když se pak navracoval Jozafat král Judský do domu svého v pokoji do Jeruzaléma,
Sa’ad da Yehoshafat sarkin Yahuda ya dawo zuwa fadansa a Urushalima lafiya,
2 Vyšel jemu vstříc Jéhu syn Chananův, prorok, a řekl králi Jozafatovi: Zdaliž jsi bezbožnému měl pomáhati, a ty, jenž nenávidí Hospodina, milovati? Z té příčiny proti tobě jest hněv Hospodinův.
Yehu mai duba, ɗan Hanani, ya fita don yă tarye shi, ya kuma ce wa sarki, “Ya yi kyau ke nan da ka taimaki mugu ka kuma ƙaunaci waɗanda suke ƙin Ubangiji? Da yake ka yi haka fushin Ubangiji yana a kanka
3 Ale však nalezly se věci dobré při tobě, že jsi vysekal háje z země, a nastrojil srdce své, abys hledal Boha.
Duk da haka an sami wani abin kirki a wurinka, gama ka kawar da ginshiƙan Ashera a ƙasar, ka kuma sa zuciyarka a kan neman Allah.”
4 I bydlil Jozafat v Jeruzalémě, a zase projel lid od Bersabé až k hoře Efraim, a navrátil je k Hospodinu Bohu otců jejich.
Yehoshafat ya zauna a Urushalima, ya kuma fita yana shiga cikin mutane daga Beyersheba zuwa ƙasar tudun Efraim ya kuma juyar da su ga Ubangiji Allah na kakanninsu.
5 A ustanovil soudce v zemi po všech městech Judských hrazených, v jednom každém městě.
Ya naɗa alƙalai a kowanne daga cikin biranen katanga na Yahuda a ƙasar.
6 Tedy řekl soudcům: Vizte, jak co činíte; nebo nevedete soudu za člověka, ale za Hospodina, kterýž vám přítomen jest při vykonávání soudu.
Ya faɗa musu, “Ku lura da abin da kuke yi, gama shari’ar da kuke yi ba ta mutum ba ce, amma ta Ubangiji ce, yana tare da ku sa’ad da kuke yanke shari’a.
7 A protož budiž bázeň Hospodinova při vás. Ostříhejte toho a čiňte tak, neboť není u Hospodina Boha našeho nepravosti, tak aby šetřiti měl osob, aneb přijímati dary.
Yanzu fa ku ji tsoron Ubangiji. Ku yi hankali a kan abin da kuke yi, gama Ubangiji Allahnmu ba ya sonkai ko nuna wariya ko cin hanci.”
8 Tak i v Jeruzalémě ustanovil Jozafat některé z Levítů a z kněží, a z knížat otcovských, čeledí Izraelských, k soudu Hospodinovu a k rozepřem těch, kteříž by se obraceli o to do Jeruzaléma.
A Urushalima kuma, Yehoshafat ya naɗa waɗansu Lawiyawa, firistoci da kawunan iyalan Isra’ilawa don su tabbatar da an bi dokar Ubangiji, su kuma sasanta tsakanin mutane. A Urushalima za su zauna.
9 A přikázal jim, řka: Takž dělejte v bázni Hospodinově, u víře a v srdci upřímém.
Ya ba su waɗannan umarnai, “Ku yi aikinku da aminci da tsoron Ubangiji da dukan zuciyarku.
10 A při všeliké rozepři, kteráž by přišla před vás od bratří vašich, kteříž bydlí v městech svých, buď mezi krví a krví, mezi zákonem a přikázaním, ustanoveními a soudy, napomenete jich, aby nehřešili proti Hospodinu, tak aby nepřišla prchlivost na vás, ani na bratří vaše. Tak čiňte, a neuběhnete v hřích.
Cikin kowane batun da ya zo gabanku daga’yan’uwanku waɗanda suke zama a birane, ko batun na kisa ne ko kuwa waɗansu batuttuwan da suka shafi doka, umarnai, ƙa’idodi ko farillai, dole ku ja musu kunne kada su yi wa Ubangiji zunubi; in ba haka ba fushinsa zai sauko a kanku da’yan’uwanku. Ku yi wannan, ta haka ba za ku kuwa yi zunubi ba.
11 A aj, Amariáš, kněz nejvyšší, mezi vámi bude ve všech věcech Hospodinových, a Zebadiáš syn Izmaelův, vývoda domu Judova, ve všeliké věci královské. Máte také Levíty správce mezi sebou; posilňtež se a zmužile sobě počínejte, a budeť Hospodin s tím, kdož bude dobrý.
“Amariya, babban firist, shi ne zai shugabance ku a kan dukan al’amuran da suke na wajen Ubangiji, Zebadiya ɗan Ishmayel kuwa, shugabanku a kan dukan al’amuran da suka shafi sarki, Lawiyawa kuma za su zama a matsayin manya a gabanku. Ku yi abubuwa da ƙarfin hali, bari kuma Ubangiji yă kasance tare da masu yin gaskiya.”

< 2 Kronická 19 >