< 1 Samuelova 8 >

1 Když se pak zstaral Samuel, ustanovil syny své za soudce v Izraeli.
Da Sama’ila ya tsufa, sai ya naɗa’ya’yansa maza su zama alƙalan Isra’ila.
2 A bylo jméno syna jeho prvorozeného Joel, a jméno druhého Abia; ti byli soudcové v Bersabé.
Sunan ɗansa na fari Yowel, na biyu kuwa Abiya. Suka yi alƙalanci a Beyersheba.
3 Nechodili pak synové jeho po cestách jeho, ale uchýlili se po lakomství, a berouce dary, převraceli soud.
Amma’ya’yansa ba su bi hanyar mahaifinsu ba. Suka mai da hankalinsu ga neman kuɗi da cin hanci, suna kuma danne gaskiya.
4 Shromáždili se tedy všickni starší Izraelští, a přišli k Samuelovi do Ramata.
Sai dukan shugabannin Isra’ila suka taru suka zo wurin Sama’ila a Rama.
5 A řekli jemu: Aj, tys se již zstaral, a synové tvoji nechodí po cestách tvých; protož nyní ustanov nám krále, aby soudil nás, jakož jest u všech národů.
Suka ce masa, “Ka tsufa,’ya’yanka kuma ba sa bin hanyarka, saboda haka sai ka naɗa sarkin da zai bi da mu kamar yadda sauran ƙasashe suke da su.”
6 I nelíbila se ta řeč Samuelovi, že řekli: Dej nám krále, aby nás soudil. Protož modlil se Samuel Hospodinu.
Amma Sama’ila bai ji daɗi sa’ad da suka ce, “Ka ba mu sarki da zai bi da mu.” Sai ya yi addu’a ga Ubangiji.
7 Tedy řekl Hospodin Samuelovi: Uposlechni hlasu lidu ve všem, což mluví tobě; nebo ne tebouť jsou pohrdli, ale mnou pohrdli, abych nekraloval nad nimi.
Ubangiji kuwa ya ce masa, “Ka saurari dukan maganganun da mutanen suke gaya maka. Ai, ba kai ba ne suka ƙi, ni ne suka ƙi in zama sarkinsu.
8 Podlé všech skutků těch, kteréž činili od onoho dne, v němž jsem je vyvedl z Egypta až do tohoto dne, kdyžto opustili mne, a sloužili bohům cizím, takť oni činí i tobě.
Haka suka yi daga tun daga ranar da na fitar da su daga Masar har zuwa yau, suka ƙi ni, suka bauta wa waɗansu alloli, haka ma suke yi maka.
9 Protož nyní uposlechni hlasu jejich, a však nejprv osvědč pilně před nimi, a oznam jim obyčej krále, kterýž nad nimi kralovati bude.
Yanzu ka saurare su amma ka yi musu kashedi sosai, ka sa su san abin da sarkin da zai bi da su zai yi.”
10 I mluvil Samuel všecky řeči Hospodinovy k lidu, kteříž krále žádali od něho.
Sama’ila kuwa ya ce wa mutanen da suke roƙo yă naɗa musu sarki dukan abin da Ubangiji ya faɗa.
11 A řekl: Tento bude obyčej krále, kterýž kralovati bude nad vámi: Bráti bude syny vaše, a dá je k vozům svým, a zdělá sobě z nich jezdce, a běhati budou před vozem jeho.
Ya ce musu, “Ga abin da sarkin da zai yi mulkinku zai yi. Zai kwashe’ya’yanku yă sa su yi aiki da kekunan yaƙi da dawakansa, waɗansu za su riƙa gudu a gaban keken yaƙinsa.
12 Také ustanoví je sobě za hejtmany nad tisíci a za padesátníky, a aby jemu orali rolí jeho, a žali obilé jeho, též aby jemu dělali nástroje válečné a přípravy k vozům jeho.
Zai sa waɗansu su zama shugabannin mutum dubu-dubu da kuma na hamsin-hamsin. Waɗansu za su yi masa noma da girbi. Waɗansu za su ƙera masa makaman yaƙi da kayayyaki don keken yaƙinsa.
13 Dcery také vaše bráti bude, aby dělaly masti, a byly kuchařky a pekařky.
Zai sa’ya’yanku mata yin aikin turare da dafe-dafe da kuma toye-toye.
14 Nadto pole vaše a vinice vaše, i olivoví vaše nejvýbornější pobéře a rozdá služebníkům svým.
Zai karɓi gonakinku mafi kyau da gonakin inabinku da gonakin zaitunku yă ba wa ma’aikatansa.
15 Také z toho, což vsejete, a z vinic vašich desátky bráti bude, a dá komorníkům a služebníkům svým.
Zai kuma karɓi zakan hatsinku da na inabinku yă ba shugabannin fadarsa da sauran masu hidimarsa.
16 Též služebníky vaše a děvky vaše, a mládence vaše nejzpůsobnější, i osly vaše vezme, aby jimi dělal dílo své.
Zai ƙwace bayinku maza da mata, da shanunku, da jakunanku mafi kyau domin su yi masa aiki.
17 Z stád vašich desátky bráti bude, a vy budete jemu za služebníky.
Zai karɓi zakan dabbobinku, ku kanku za ku zama bayinsa.
18 I budete volati v ten den příčinou krále vašeho, kteréhož byste sobě vyvolili, a nevyslyší vás Hospodin dne toho.
Sa’ad da ranar ta zo, za ku yi kuka ku nemi a fishe ku daga sarkin da kuka zaɓa, Ubangiji kuwa ba zai ji ku ba.”
19 Nechtěl však lid uposlechnouti řeči Samuelovy, a řekli: Nikoli, ale král bude nad námi,
Amma mutanen suka ƙi jin Sama’ila, sai suka ce, “A’a, mu dai, muna son sarki yă bi da mu.”
20 Abychom i my také byli, jako všickni jiní národové, a souditi nás bude král náš, a vycházeje před námi, bojovati bude za nás.
Ta haka za mu zama kamar sauran ƙasashe, mu kasance da sarkin da zai bi da mu, yă tafi tare da mu zuwa yaƙe-yaƙe.
21 Vyslyšev tedy Samuel všecka slova lidu, oznámil je Hospodinu.
Da Sama’ila ya ji duk maganganun da mutanen suka faɗa, sai ya mayar wa Ubangiji.
22 I řekl Hospodin Samuelovi: Uposlechni hlasu jejich, a ustanov jim krále. Protož řekl Samuel mužům Izraelským: Jdětež jeden každý do města svého.
Ubangiji kuwa ya ce, “Ka saurare su, ka naɗa masu sarki.” Sa’an nan Sama’ila ya ce wa mutanen Isra’ila, “Kowa yă koma garinsa.”

< 1 Samuelova 8 >