< Žalmy 94 >
1 Bože silný pomst, Hospodine, Bože silný pomst, zastkvěj se.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Zdvihni se, ó soudce vší země, a dej odplatu pyšným.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 Až dokud bezbožní, Hospodine, až dokud bezbožní budou plésati,
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 Žváti a hrdě mluviti, honosíce se, všickni činitelé nepravosti?
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 Lid tvůj, Hospodine, potírati a dědictví tvé bědovati?
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 Vdovy a příchozí mordovati, a sirotky hubiti,
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 Říkajíce: Nehledíť na to Hospodin, aniž tomu rozumí Bůh Jákobův?
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Rozumějte, ó vy hovadní v lidu, a vy blázni, kdy srozumíte?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 Zdali ten, jenž učinil ucho, neslyší? A kterýž stvořil oko, zdali nespatří?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 Zdali ten, jenž tresce národy, nebude kárati, kterýž učí lidi umění?
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 Hospodinť zná myšlení lidská, že jsou pouhá marnost.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Blahoslavený jest ten muž, kteréhož ty cvičíš, Hospodine, a z zákona svého jej vyučuješ.
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 Abys mu způsobil pokoj před časy zlými, až by za tím vykopána byla bezbožníku jáma.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 Neboť neopustí Hospodin lidu svého, a dědictví svého nezanechá,
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 Ale až k spravedlnosti navrátí se soud, a za ním všickni upřímého srdce.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Kdož by se byl o mne zasadil proti zlostníkům? Kdo by se byl za mne postavil proti těm, jenž páší nepravost?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Kdyby mi Hospodin nebyl ku pomoci, tudíž by se byla octla duše má v mlčení.
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 Již jsem byl řekl: Klesla noha má, ale milosrdenství tvé, ó Hospodine, zdrželo mne.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 Ve množství přemyšlování mých u vnitřnosti mé, tvá potěšování obveselovala duši mou.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Zdaliž se k tobě přitovaryší stolice převráceností těch, jenž vynášejí nátisk mimo spravedlnost,
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 Jenž se shlukují proti duši spravedlivého, a krev nevinnou odsuzují?
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 Ale Hospodin jest mým hradem vysokým, a Bůh můj skalou útočiště mého.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 Onť obrátí na ně nepravost jejich, a zlostí jejich zahladí je, zahladí je Hospodin Bůh náš.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.