< Žalmy 50 >
1 Žalm Azafovi. Bůh silný, Bůh Hospodin mluvil, a přivolal zemi od východu slunce i od západu jeho.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Z Siona v dokonalé kráse Bůh zastkvěl se.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Béřeť se Bůh náš, a nebude mlčeti; oheň před ním vše zžírati bude, a vůkol něho vichřice náramná.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 Zavolal nebes s hůry i země, aby soudil lid svůj, řka:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 Shromažďte mi svaté mé, kteříž smlouvu se mnou učinili při obětech.
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 I budou vypravovati nebesa spravedlnost jeho; nebo sám Bůh soudce jest. (Sélah)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 Slyš, lide můj, a buduť mluviti, Izraeli, a buduť tebou osvědčovati. Já zajisté Bůh, Bůh tvůj jsem.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 Nechci tě obviňovati z příčiny obětí tvých, ani zápalů tvých, že by vždycky přede mnou nebyli.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 Nevezmuť z domu tvého volka, ani z chlévů tvých kozlů.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 Nebo má jest všecka zvěř lesní, i hovada na tisíci horách.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 Já znám všecko ptactvo po horách, a zvěř polní před sebou mám.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 Zlačním-li, nic tobě o to nedím; nebo můj jest okršlek zemský i plnost jeho.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Zdaliž jídám maso z volů, a pijím krev kozlovou?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Obětuj Bohu obět chvály, a plň Nejvyššímu své sliby;
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 A vzývej mne v den ssoužení, vytrhnu tě, a ty mne budeš slaviti.
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 Sic jinak bezbožníku praví Bůh: Což tobě do toho, že ty vypravuješ ustanovení má, a béřeš smlouvu mou v ústa svá,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 Poněvadž jsi vzal v nenávist kázeň, a zavrhl jsi za sebe slova má.
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 Vidíš-li zloděje, hned s ním běžíš, a s cizoložníky díl svůj máš.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 Ústa svá pouštíš ke zlému, a jazyk tvůj skládá lest.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 Usazuješ se, a mluvíš proti bratru svému, a na syna matky své lehkost uvodíš.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 To jsi činil, a já mlčel jsem. Měl-liž jsi ty se domnívati, že já tobě podobný budu? Nýbrž trestati tě budu, a představímť to před oči tvé.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 Srozumějtež tomu již aspoň vy, kteříž se zapomínáte na Boha, abych snad nepochytil, a nebyl by, kdo by vytrhl.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Kdož obětuje obět chvály, tenť mne uctí, a tomu, kdož napravuje cestu svou, ukáži spasení Boží.
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”