< Žalmy 1 >

1 Blahoslavený ten muž, kterýž nechodí po radě bezbožných, a na cestě hříšníků nestojí, a na stolici posměvačů nesedá.
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 Ale v zákoně Hospodinově jest líbost jeho, a v zákoně jeho přemýšlí dnem i nocí.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 Nebo bude jako strom štípený při tekutých vodách, kterýž ovoce své vydává časem svým, jehožto list nevadne, a cožkoli činiti bude, šťastně mu se povede.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 Ne takť budou bezbožní, ale jako plevy, kteréž rozmítá vítr.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 A protož neostojí bezbožní na soudu, ani hříšníci v shromáždění spravedlivých.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 Neboť zná Hospodin cestu spravedlivých, ale cesta bezbožných zahyne.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.

< Žalmy 1 >