< 4 Mojžišova 19 >
1 I mluvil Hospodin k Mojžíšovi a k Aronovi, řka:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
2 Toto jest ustanovení zákona, kteréž přikázal Hospodin, řka: Mluv k synům Izraelským, ať vezmouce, přivedou k tobě jalovici červenou bez vady, na níž by nebylo poškvrny, a na kterouž by ještě jho nebylo kladeno.
“Wannan ita ce ƙa’ida wadda Ubangiji ya umarta. Faɗa wa Isra’ilawa su kawo maka jan karsana marar lahani, ko marar aibi wadda ba a taɓa sa ta tă yi noma ba.
3 A dáte ji Eleazarovi knězi, kterýž vyvede ji ven z stanů, a rozkáže ji zabiti před sebou.
Ka ba wa Eleyazar firist; a kuma kai ta bayan sansani, a yanka a gaban Eleyazar.
4 A vezma Eleazar kněz krve její na prst svůj, kropiti bude jí naproti stánku úmluvy sedmkrát.
Sa’an nan Eleyazar firist zai ɗiba jininta a yatsarsa, yă yayyafa sau bakwai wajen gaban Tentin Sujada.
5 Potom káže tu jalovici spáliti před očima svýma; kůži její, i maso její, i krev její s lejny jejími dá spáliti.
Sa’an nan a ƙone dukan karsanar, haɗe da fatarta, naman, jinin da kayan cikin, yayinda Eleyazar yake kallo.
6 A vezma kněz dřeva cedrového, yzopu a červce dvakrát barveného, uvrže to vše do ohně, v kterémž ta jalovice hoří.
Firist zai ɗauki itacen al’ul, da hizzob, da jan ulu, yă jefa su a kan karsanar da ake ƙonewa.
7 I zpéře kněz roucha svá, a tělo své umyje vodou; potom vejde do stanů, a bude nečistý až do večera.
Bayan haka, dole firist yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka. Sa’an nan zai iya shiga cikin sansani, amma zai kasance da ƙazanta har yamma.
8 Takž také i ten, kterýž ji pálil, zpéře roucha svá u vodě, a tělo své obmyje vodou, a nečistý bude až do večera.
Dole mutumin da ya ƙone ta yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka, shi ma zai kasance da ƙazanta har yamma.
9 Popel pak té jalovice spálené smete muž čistý, a vysype jej vně za stany na místě čistém, aby byl všechněm synům Izraelským chován k vodě očištění, kteráž bude k očištění za hřích.
“Mutumin da yake da tsarki, zai tara tokar karsanar, yă sa ta a wurin da yake da tsabta a bayan sansani. Jama’ar Isra’ilawa ne za su adana shi don amfani a ruwan tsabtaccewa; wannan domin tsarkakewa ne daga zunubi.
10 A ten, kdož by smetl popel té jalovice, zpéře roucha svá a nečistý bude až do večera. A budou to míti synové Izraelští i příchozí, kterýž jest pohostinu u prostřed nich, za ustanovení věčné.
Dole mutumin da ya tara tokar karsanar yă wanke rigunarsa, zai kuwa kasance da ƙazanta har yamma. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla ta har abada ga Isra’ilawa, da kuma baƙin da suke zama a cikinsu.
11 Kdo by se dotkl těla kteréhokoli mrtvého člověka, nečistý bude za sedm dní.
“Duk wanda ya taɓa gawa, zai kasance da ƙazanta har kwana bakwai.
12 Takový očišťovati se bude tou vodou dne třetího a dne sedmého, i bude čistý; neočistí-li se pak dne třetího a dne sedmého, nebudeť čistý.
Dole yă tsarkake kansa da ruwa a rana ta uku, da kuma a rana ta bakwai; sa’an nan zai zama da tsarki. Amma in bai tsarkake kansa a rana ta uku da kuma a rana ta bakwai ba, ba zai kasance da tsarki ba.
13 Kdo by koli, dotkna se těla mrtvého člověka, kterýž umřel, neočistil se, příbytku Hospodinova poškvrnil. Protož vyhlazena bude duše ta z Izraele, nebo vodou očišťování není pokropen; nečistýť bude, a nečistota jeho zůstává na něm.
Duk wanda ya taɓa gawar wani, bai kuma tsarkake kansa ba, ya ƙazantar da tabanakul na Ubangiji ke nan. Dole a ware wannan mutum daga cikin Isra’ilawa. Gama ba a yayyafa ruwan tsabtaccewa a kansa ba; ya ƙazantu, ya kasance da ƙazanta ke nan.
14 Tento jest také zákon, kdyby člověk umřel v stanu: Kdo by koli všel do toho stanu, a kdo by koli byl v stanu, nečistý bude za sedm dní.
“Ga ƙa’idar da za a bi in mutum ya mutu a cikin tenti. Duk wanda ya shiga tentin, kuma duk wanda yake cikinsa, za su zama da ƙazanta har kwana bakwai,
15 Tolikéž všeliká nádoba odkrytá, kteráž by neměla svrchu přikryvadla na sobě, nečistá bude.
kuma kowane abin da ake zuba kaya, wanda ba shi da murfi a kansa, zai zama da ƙazanta.
16 Tak kdož by se koli dotkl na poli buď mečem zabitého, aneb mrtvého, buďto kosti člověka, aneb hrobu, nečistý bude za sedm dní.
“Wanda duk yake a fili, ya kuma taɓa gawa wanda aka kashe da takobi, ko wanda ya mutu mutuwar Allah, ko ƙashin mutum, ko kabari, zai ƙazantu har bakwai.
17 A vezmou pro nečistého popela z spálené za hřích, a nalejí na něj vody živé do nádoby.
“Ga wanda ya ƙazantu kuwa, a ɗiba toka daga hadaya ta ƙonawa ta tsarkakewa, a zuba a cikin tulu, sa’an nan a zuba ruwa mai gudu a kansu.
18 Potom vezme člověk čistý yzopu, a omočí jej v té vodě, a pokropí stanu, i všeho nádobí i lidí, kteříž by tu byli, tolikéž toho, kterýž dotkl se kosti, aneb zabitého, aneb mrtvého, aneb hrobu.
Sa’an nan wanda yake tsarkakakke, zai ɗauki hizzob yă tsoma a ruwa, yă yayyafa a tentin da dukan kayayyakinsa, da kuma a kan mutanen da suke wurin. Dole kuma yă yayyafa ruwan a kan duk wanda ya taɓa ƙashin mutu, ko kabari, ko kuma wanda aka kashe, ko wanda ya yi mutuwa ta Allah.
19 Pokropí tedy čistý nečistého v den třetí a v den sedmý; a když jej očistí dne sedmého, zpéře šaty své, a umyje se vodou, a čistý bude u večer.
A rana ta uku, da ta bakwai kuma mai tsarkakewa zai yayyafa wa marar tsarkin ruwa, a rana ta bakwai kuma yă tsarkake shi. Wanda aka tsarkaken kuwa, dole yă wanke rigunarsa, yă kuma yi wanka da yamma, zai kuma tsarkaka.
20 Jestliže by pak kdo nečistý jsa, neočistil se, vyhlazena bude duše ta z prostředku shromáždění; nebo svatyně Hospodinovy poškvrnil, vodou očišťování nejsa pokropen; nečistý jest.
Amma in wanda yake da ƙazanta bai tsarkake kansa ba, dole a ware shi daga cikin jama’a, domin ya ƙazantar da wuri mai tsarki na Ubangiji. Ba a yayyafa masa ruwa na tsarkakewa ba, ya zama da ƙazanta.
21 I bude jim to za ustanovení věčné. Kdož by pak tou vodou očišťování kropil, zpéře roucha svá, a kdož by se dotkl vody očišťování, nečistý bude až do večera.
Wannan za tă zama musu dawwammamiyar farilla. “Mutumin da ya yayyafa ruwa na tsarkakewa, shi ma dole yă wanke rigarsa. Duk wanda kuma ya taɓa ruwan tsarkakewa, zai kasance da ƙazanta har yamma.
22 Čehokoli dotkl by se nečistý, nečisté bude; člověk také, kterýž by se dotkl toho, nečistý bude až do večera.
Duk abin da mai ƙazanta ya taɓa, ya ƙazantu, kowa kuma ya taɓa wannan abu, ya ƙazantu ke nan, har yamma.”