< Matouš 20 >
1 Nebo podobno jest království nebeské člověku hospodáři, kterýž vyšel na úsvitě, aby najal dělníky na vinici svou.
“Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa.
2 Smluviv pak s dělníky z peníze denního, odeslal je na vinici svou.
Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.
3 A vyšed okolo hodiny třetí, uzřel jiné, ani stojí na trhu zahálejíce.
“Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome.
4 I těm řekl: Jdětež i vy na vinici, a co bude spravedlivého, dám vám.
Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’
5 A oni šli. Opět vyšed při šesté a deváté hodině, učinil též.
Saboda haka suka tafi. “Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka.
6 Při jedenácté pak hodině vyšed, nalezl jiné, ani stojí zahálejíce. I řekl jim: Pročež tu stojíte, celý den zahálejíce?
Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’
7 Řkou jemu: Nebo nižádný nás nenajal. Dí jim: Jdětež i vy na vinici, a což by bylo spravedlivého, vezmete.
“Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’ “Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’
8 Večer pak řekl pán vinice šafáři svému: Zavolej dělníků a zaplať jim, počna od posledních až do prvních.
“Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’
9 A přišedše ti při jedenácté hodině najatí, vzali jeden každý po penízi.
“Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda.
10 Přišedše pak první, domnívali se, že více vezmou, ale vzali i oni jeden každý po penízi.
Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda.
11 A vzavše, reptali proti hospodáři,
Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar.
12 Řkouce: Tito poslední jednu hodinu dělali, a rovné jsi je nám učinil, kteříž jsme nesli břímě dne i horko.
Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’
13 On pak odpovídaje, řekl jednomu z nich: Příteli, nečiním tobě křivdy. Zdaliž jsi z peníze nesmluvil se mnou?
“Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba?
14 Vezmiž, což tvého jest, a jdi předce, já pak chci tomuto poslednímu dáti jako i tobě.
Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka.
15 Zdaliž mi nesluší v mém učiniti, což chci? Čili oko tvé nešlechetné jest, že já dobrý jsem?
Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’
16 Takť budou poslední první, a první poslední; nebo mnoho jest povolaných, ale málo vyvolených.
“Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”
17 A vstupuje Ježíš do Jeruzaléma, pojal dvanácte učedlníků soukromí na cestě. I řekl jim:
To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu,
18 Aj, vstupujeme do Jeruzaléma, a Syn člověka vydán bude předním kněžím a zákonníkům, a odsoudí ho na smrt.
“Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa
19 A vydadíť jej pohanům ku posmívání a k zbičování a ukřižování, ale třetího dne z mrtvých vstane.
za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”
20 Tehdy přistoupila k němu matka synů Zebedeových s syny svými, klanějici se a proseci něco od něho.
Sai mahaifiyar’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.
21 Kterýž řekl jí: Co chceš? Řekla jemu: Rci, ať tito dva synové moji sedají, jeden po pravici tvé a druhý po levici, v království tvém.
Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?” Ta ce, “Ka sa daga cikin’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”
22 Odpovídaje pak Ježíš, řekl: Nevíte, zač prosíte. Můžete-li píti kalich, kterýž já píti budu, a křtem, jímž já se křtím, křtěni býti? Řekli jemu: Můžeme.
Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?” Suka amsa, “Za mu iya.”
23 Dí jim: Kalich zajisté můj píti budete, a křtem, jímž já se křtím, pokřtěni budete, ale seděti po pravici mé a po levici mé, neníť mé dáti, ale těm, kterýmž připraveno jest od Otce mého.
Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”
24 A uslyšavše to deset jiných, rozhněvali se na ty dva bratry.
Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da’yan’uwan nan biyu.
25 Ale Ježíš svolav je, řekl: Víte, že knížata národů panují nad nimi, a kteříž velicí jsou, moci užívají nad nimi.
Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko.
26 Ale ne tak bude mezi vámi. Nýbrž kdožkoli chtěl by mezi vámi býti velikým, budiž služebník váš.
Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku,
27 A kdož by koli mezi vámi chtěl býti přední, budiž váš služebník;
kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku,
28 Jako i Syn člověka nepřišel, aby jemu slouženo bylo, ale aby on sloužil, a aby dal život svůj mzdu na vykoupení za mnohé.
kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
29 A když vycházeli z Jericho, šel za ním zástup veliký.
Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi.
30 A aj, dva slepí sedící u cesty, uslyšavše, že by Ježíš tudy šel, zvolali, řkouce: Smiluj se nad námi, Pane, synu Davidův.
Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
31 Zástup pak přimlouval jim, aby mlčeli. Oni pak více volali, řkouce: Smiluj se nad námi, Pane, synu Davidův.
Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”
32 I zastaviv se Ježíš, zavolal jich, a řekl: Co chcete, abych vám učinil?
Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”
33 Řkou jemu: Pane, ať se otevrou oči naše.
Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”
34 I slitovav se nad nimi Ježíš, dotekl se očí jejich, a hned prohlédly oči jejich. I šli za ním.
Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.