< Lukáš 2 >
1 I stalo se v těch dnech, vyšlo poručení od císaře Augusta, aby byl popsán všecken svět.
Ananan cikin kwanakin, sai Kaisar Augustas ya yi shela ya umarta a kidaya dukan mutane da ke zaune a cikin duniya.
2 (To popsání nejprvé stalo se, když vládařem Syrským byl Cyrenius.)
Wannan itace kidaya ta farko da aka yi lokacin da Kiriniyus yake mulkin Suriya.
3 I šli všickni, aby zapsáni byli, jeden každý do svého města.
Sabili da haka, kowa ya koma garinsa domin a yi masa rijista domin kidayan.
4 Vstoupil pak i Jozef od Galilee z města Nazarétu do Judstva, do města Davidova, kteréž slove Betlém, (proto že byl z domu a z čeledi Davidovy, )
Yusufu kuma ya tashi ya bar birnin Nazarat zuwa garin Baitalami da ke Yahudiya, wanda ake kuma kira birnin Dauda, domin shi daga zuriyar iyalin Dauda ne.
5 Aby zapsán byl s Marií, zasnoubenou sobě manželkou těhotnou.
Ya je can ya yi rijista tare da Maryamu, wadda yake tashi tana kuma da juna biyu.
6 I stalo se, když tam byli, naplnili se dnové, aby porodila.
Ya zama sa'adda suke can, lokaci ya yi da za ta haifi danta.
7 I porodila Syna svého prvorozeného, a plénkami ho obvinula, a položila jej v jeslech, proto že neměli místa v hospodě.
Ta haifi da, dan farinta kuwa, ta nade shi da kyau da 'yan tsummoki. Ta sa shi cikin wani kwami na dabbobi, gama babu daki dominsu a masaukin.
8 A pastýři byli v krajině té, ponocujíce, a stráž noční držíce nad svým stádem.
A cikin wannan yankin, akwai makiyaya wadanda suke zama a sarari suna tsaron garken tumakinsu da dare.
9 A aj, anděl Páně postavil se podlé nich, a sláva Páně osvítila je. I báli se bázní velikou.
Nan da nan, sai mala'ikan Ubangiji ya bayyana gare su, daukakar Ubangiji kuma ta haskaka kewaye da su, sai suka figita kwarai.
10 Tedy řekl jim anděl: Nebojtež se; nebo aj, zvěstuji vám radost velikou, kteráž bude všemu lidu.
Sai mala'ikan ya ce masu, “Kada ku ji tsoro, domin na kawo maku labari mai dadi da zai kawo murna da yawa ga dukan mutane.
11 Nebo narodil se vám dnes spasitel, kterýž jest Kristus Pán, v městě Davidově.
Yau an haifi maku mai ceto a cikin birnin Dauda! Shine Almasihu Ubangiji!
12 A toto vám bude za znamení: Naleznete nemluvňátko plénkami obvinuté, ležící v jeslech.
Wannan itace alama da za a ba ku. Za ku ga dan jariri nade cikin 'yan tsummoki kwance cikin kwamin dabbobi.”
13 A hned s andělem zjevilo se množství rytířstva nebeského, chválících Boha a řkoucích:
Nan take, sai ga babban taro daga sama tare da mala'ikan suna yabon Allah, suna cewa,
14 Sláva na výsostech Bohu, a na zemi pokoj, lidem dobrá vůle.
“Daukaka ga Allah daga bisa, bari salama ta kasance a duniya tsakanin mutanen da ya ke jin dadinsu.”
15 I stalo se, jakž odešli od nich andělé do nebe, že ti pastýři řekli vespolek: Poďme až do Betléma, a vizme tu věc, kteráž se stala, o níž Pán oznámil nám.
Ya zama sa'adda mala'iku suka bar su zuwa cikin sama, sai makiyayan su ka ce wa junansu, “Bari mu je Baitalami mu ga wannan abin da ya faru, wanda Ubangiji ya nuna mana.”
16 I přišli, chvátajíce, a nalezli Marii a Jozefa, i to nemluvňátko ležící v jeslech.
Su ka yi hamzari suka tafi can sun iske Maryamu da Yusufu, suka ga jaririn kuwa kwance a cikin kwamin dabbobin.
17 A viděvše, rozhlašovali, což jim povědíno bylo o tom děťátku.
Bayan da sun ga wannan, suka gaya wa mutane abinda aka gaya masu game da wannan yaro.
18 I divili se všickni, kteříž slyšeli o tom, což jim bylo mluveno od pastýřů.
Dukan wadanda su ka ji, su ka yi mamaki kwarai game da abin da makiyayan su ka gaya masu.
19 Ale Maria zachovávala všecky věci tyto, skládajici je v srdci svém.
Amma ita Maryamu ta ci gaba da tunani akan wadanan abubuwa da ta ji, tana tunani mai zurfi a cikin zuciyarta.
20 I navrátili se pastýři, velebíce a chválíce Boha ze všeho, což slyšeli a viděli, tak jakž bylo jim povědíno.
Makiyayan suka koma suna ta daukaka da yabon Allah domin dukan abubuwan da suka ji, suka kuma gani, dadai da yadda aka gaya masu.
21 A když se naplnilo dní osm, aby obřezáno bylo to děťátko, i nazváno jest jméno jeho Ježíš, kterýmž bylo nazváno od anděla, prvé než se v životě počalo.
Da ya kai kwana takwas, lokacin da za a yi wa jaririn kaciya, sai aka rada masa suna Yesu, sunan da mala'ikan ya bashi kamin a yi cikinsa.
22 A když se naplnili dnové očišťování Marie podlé zákona Mojžíšova, přinesli jej do Jeruzaléma, aby ho postavili Pánu,
Da kwanakin tsarkakewar su ya wuce bisa ga shari'ar Musa, Yusufu da Maryamu suka kawo shi cikin haikali a Urushalima dominsu mika shi ga Ubangiji.
23 (Jakož psáno jest v zákoně Páně, že každý pacholík, otvíraje život, svatý Pánu slouti bude, )
Kamar yadda aka rubuta a dokokin Ubangiji, “Za a kira duk da na fari kebabbe ga Ubangiji.”
24 A aby dali obět, jakož povědíno jest v zákoně Páně, dvě hrdličky aneb dvé holoubátek.
Suka kuma zo su mika hadaya bisa ga yadda aka fada a shari'ar Ubangiji, “Kurciyoyi biyu ko 'yan tantabaru biyu.”
25 A aj, byl člověk v Jeruzalémě, jemuž jméno Simeon. A člověk ten byl spravedlivý a nábožný, očekávající potěšení Izraelského, a Duch svatý byl v něm.
Ga shi akwai wani mutum a Ushalima mai suna Siman. Wannan mutum adali ne kuma mai ibada. Yana jiran mai ta'aziyar Isra'ila, kuma Ruhu Mai-sarki na bisansa.
26 A bylo jemu zjeveno od Ducha svatého, že neuzří smrti, až by prvé uzřel Krista Páně.
An kuma bayyana masa ta wurin Ruhu Mai-tsarki cewa ba zai mutu ba sai ya ga Kristi na Ubangiji.
27 Ten přišel, ponuknut byv od Ducha, do chrámu. A když uvodili rodičové Ježíše děťátko, aby učinili podlé obyčeje zákona při něm,
Wata rana Siman ya zo cikin haikali ta wurin jagorar Ruhu Mai-tsarki. Da iyayen suka kawo yaron ciki, wato Yesu, domin su cika sharudan da shari'ar ke bukata,
28 Tedy on vzal jej na lokty své, i chválil Boha a řekl:
sai Siman ya karbe shi cikin hanuwansa, ya yabi Allah ya ce,
29 Nyní propouštíš služebníka svého, Pane, podlé slova svého, v pokoji.
“Yanzu bari bawanka ya tafi da salama, Ubangiji, bisa ga kalmarka.
30 Nebo viděly oči mé spasení tvé,
Domin idanuna sun ga cetonka,
31 Kteréž jsi připravil před oblíčejem všech lidí,
wanda ka shirya a gaban dukan mutane:
32 Světlo k zjevení národům, a slávu lidu tvého Izraelského.
Haske ne na wahayi ga al'ummai, kuma daukakar mutanenka Isra'ila.”
33 Otec pak a matka jeho divili se těm věcem, kteréž praveny byly o něm.
Mahaifin yaron da Mahaifiyarsa, sun yi mamaki kwarai domin abubuwan da aka fada akansa.
34 I požehnal jim Simeon, a řekl Marii, matce jeho: Aj, položen jest tento ku pádu a ku povstání mnohým v Izraeli, a na znamení, kterémuž bude odpíráno,
Sai Siman ya albarkace su ya ce wa uwatasa Maryamu, “Ki ji da kyau, wannan yaro zai zama sanadiyar faduwa da tashin mutane dayawa a Isra'ila, kuma alama wadda ake kushen ta.
35 (A tvou vlastní duši pronikne meč, ) aby zjevena byla z mnohých srdcí myšlení.
Kuma takobi zai tsaga zuciyar ki yadda tunanin mutane za ya bayyana.”
36 Byla také Anna prorokyně, dcera Fanuelova z pokolení Asser. Ta se byla zstarala ve dnech mnohých, a živa byla s mužem sedm let od panenství svého.
Wata annabiya mai suna Annatu ta na nan wurin. Ita diyar Fanuyila ce daga kabilar Ashiru. Ta riga ta manyanta a shekaru sosai. Ta kasance da maigidanta shekaru bakwai bayan auren ta,
37 A ta vdova byla, v letech okolo osmdesáti a čtyřech, kteráž nevycházela z chrámu, posty a modlitbami sloužeci Bohu dnem i nocí.
sannan ta yi zama gwambranci na shekaru tamanin da hudu. Ba ta taba barin haikali ba, tana ci gaba da yi wa Ubangiji sujada, dare da rana.
38 A ta v touž hodinu přišedši, chválila Pána, a mluvila o něm všechněm, kteříž čekali vykoupení v Jeruzalémě.
A dadai lokacin nan, ta hau zuwa wurinsu ta fara yi wa Allah godiya. Ta gaya wa dukan wadanda ke jiran fansar Urushalima.
39 Vykonavše pak všecko podlé zákona Páně, vrátili se do Galilee, do města svého Nazaréta.
Da su ka gama komai da aka bukace su suyi bisa ga tafarkin shari'ar Ubangiji, sai suka koma Galili, zuwa birninsu, Nazarat.
40 Děťátko pak rostlo, a posilovalo se v duchu, plné moudrosti, a milost Boží byla v něm.
Yaron kuma ya yi girma ya zama da karfi, yana karuwa da hikima, alherin Ubangiji kuma yana kansa.
41 I chodívali rodičové jeho každého roku do Jeruzaléma na den slavný velikonoční.
Iyayensa sukan tafi Urushalima kowacce shekara domin idin ketarewa.
42 A když byl ve dvanácti letech, a oni vstupovali do Jeruzaléma, podlé obyčeje toho dne svátečního,
Da yana shekara goma sha biyu, suka sake haurawa daidai lokacin idin a al'adance.
43 A když vykonali ty dni, a již se navracovali, zůstalo dítě Ježíš v Jeruzalémě, a nevěděli Jozef a matka jeho.
Bayan da sun cika dukan kwanakin idin, sun fara dawowa gida. Amma dan yaron Yesu ya jinkirta ya zauna a Urushalima, kuma iyayensa basu sani ba.
44 Domnívajíce se pak o něm, že by byl v zástupu, ušli den cesty. I hledali ho mezi příbuznými a mezi známými.
Suna tsammani yana tare da sauran mutane da suke tafiya tare, sai suka yi tafiya na kwana daya. Suka fara neman sa a cikin danginsu da abokansu.
45 A nenalezše jeho, navrátili se do Jeruzaléma, hledajíce ho.
Da ba su gan shi ba, sai suka koma Urushalima suna cigiyar sa a can.
46 I stalo se po třech dnech, že nalezli jej v chrámě, an sedí mezi doktory, poslouchaje jich, a otazuje se jich.
Ya zama bayan kwanaki uku, su ka same shi a cikin haikali, yana zama a tsakiyar malamai, yana sauraron su yana kuma yi masu tambayoyi.
47 A děsili se všickni, kteříž jej slyšeli, nad rozumností a odpovědmi jeho.
Dukan wadanda suka ji shi suna ta mamakin fahimtar sa da amsoshin sa.
48 A uzřevše ho, ulekli se. I řekla matka jeho k němu: Synu, proč jsi nám tak učinil? Aj, otec tvůj a já s bolestí hledali jsme tebe.
Da suka gan shi, suka yi mamaki kwarai. Mahaifiyarsa ta ce masa, “Da na, don me ka yi mana haka? Ka ji, mahaifinka da ni muna ta neman ka rai a bace.”
49 I řekl jim: Co, že jste mne hledali? Zdaliž jste nevěděli, že v těch věcech, kteréž jsou Otce mého, musím já býti?
Ya ce masu, “Don me kuke nema na? Ba ku sani cewa dole in kasance a gidan Ubana ba?”
50 Ale oni nesrozuměli těm slovům, kteráž jim mluvil.
Amma ba su gane abin da yake nufi da kalmomin nan ba.
51 I šel s nimi, a přišel do Nazaréta, a byl poddán jim. Matka pak jeho zachovávala všecka slova ta v srdci svém.
Sa'annan ya koma gida tare da su zuwa Nazarat yana kuma masu biyayya. Mahaifiayarsa kuma ta ajiye dukan wadannan abubuwa a zuciyarta tana yin tunani akansu.
52 A Ježíš prospíval moudrostí, a věkem, a milostí, u Boha i u lidí.
Amma Yesu ya ci gaba da hikima da girma, ya kuma karu da tagomashi wurin Allah da mutane.