< Jób 35 >
1 Ještě mluvil Elihu, a řekl:
Sai Elihu ya ce,
2 Domníváš-liž se, že jsi to s soudem řekl: Spravedlnost má převyšuje Boží?
“Ko kana tsammani wannan gaskiya ne? Kana cewa, ‘Ni mai adalci ne a gaban Allah.’
3 Nebo jsi řekl: Co mi prospěje, jaký užitek budu míti, bych i nehřešil?
Duk da haka kana tambayarsa cewa, ‘Wace riba nake da ita, kuma mene ne zan samu ta wurin ƙin yin zunubi?’
4 Já odpovím tobě místně, i tovaryšům tvým s tebou.
“Zan so in ba ka amsa kai tare da abokanka.
5 Pohleď na nebe a viz, anobrž spatř oblaky, vyšší, než-lis ty.
Ku ɗaga kai ku dubi sama ku gani; ku dubi gizagizai a samanku.
6 Jestliže bys hřešil, co svedeš proti němu? A byť se i rozmnožily nešlechetnosti tvé, co mu uškodíš?
In kun yi zunubi ta yaya wannan zai shafi Allah? In zunubanku sun yi yawa, me wannan zai yi masa?
7 Budeš-li spravedlivý, čeho mu udělíš? Aneb co z ruky tvé vezme?
In kuna da adalci, me kuka ba shi, ko kuma me ya karɓa daga hannunku?
8 Každémuť člověku bezbožnost jeho uškodí, a synu člověka spravedlnost jeho prospěje.
Muguntarku takan shafi mutum kamar ku ne kaɗai, adalcinku kuma yakan shafi’yan adam ne kaɗai.
9 Z množství nátisk trpících, kteréž k tomu přivodí, aby úpěli a křičeli pro ukrutnost povýšených,
“Mutane suna kuka don yawan zalunci; suna roƙo don taimako daga hannu mai ƙarfi.
10 Žádný neříká: Kde jest Bůh stvořitel můj? Ješto on dává zpěv i v noci.
Amma ba wanda ya ce, ‘Ina Allah wanda ya halicce ni, mai ba da waƙoƙi cikin dare,
11 On vyučuje nás nad hovada zemská, a nad ptactvo nebeské moudřejší nás činí.
wanda ya fi koya mana fiye da dabbobin duniya ya kuma sa muka fi tsuntsayen cikin iska hikima.’
12 Tehdáž volají-li pro pýchu zlých, nebývají vyslyšáni.
Ba ya amsawa lokacin da mutane suka yi kira don taimako domin girman kan mugaye.
13 A jistě žeť ošemetnosti nevyslýchá Bůh silný, a Všemohoucí nepatří na ni.
Lalle Allah ba ya sauraron roƙonsu na wofi; Maɗaukaki ba ya kula da roƙonsu.
14 Mnohem méně, jestliže díš: Nepatříš na to. Sám s sebou vejdi v soud před ním, a doufej v něho.
Ta yaya zai saurara sosai ko zai saurara lokacin da kake cewa ba ka ganinsa, cewa ka kawo ƙara a wurinsa kuma dole ka jira shi.
15 Ale nyní poněvadž nic není těch věcí, navštívil jej hněv jeho; nebo nechce znáti hojnosti této veliké.
Kuma ka ce, ba ya ba da horo cikin fushinsa ko kaɗan ba ya kula da mugunta.
16 A protož marně Job otvírá ústa svá, hloupě rozmnožuje řeči své.
Saboda haka Ayuba ya buɗe baki yana magana barkatai; yana ta yawan magana ba tare da sani ba.”