< Jeremiáš 22 >

1 Takto řekl Hospodin: Sejdi do domu krále Judského, a mluv tam slovo toto,
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka gangara zuwa fadan sarkin Yahuda ka yi shelar wannan saƙo a can ka ce,
2 A rci: Slyš slovo Hospodinovo, králi Judský, kterýž sedíš na stolici Davidově, ty i služebníci tvoji i lid tvůj, kteříž chodíte skrze brány tyto.
‘Ka ji maganar Ubangiji, ya sarkin Yahuda, kai da kake zaune kan gadon sarautar Dawuda, kai, da fadawanka da mutanenka waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi.
3 Takto praví Hospodin: Konejte soud a spravedlnost, a vychvacujte obloupeného z ruky násilníka; příchozímu tolikéž, sirotku, ani vdově nečiňte křivdy, aniž jich utiskujte, a krve nevinné nevylévejte na místě tomto.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka yi abin da yake gaskiya da kuma daidai. Ka kuɓutar da wannan da aka yi masa ƙwace daga hannun mai zaluntarsa. Kada ka yi abin da ba daidai ba ko ka cuci baƙo, maraya ko gwauruwa, kuma kada ka zub da jini marar laifi a wannan wuri.
4 Nebo budete-li to pilně vykonávati, jistě že poberou se skrze brány domu tohoto králové, sedící místo Davida na stolici jeho, jezdíce na vozích, neb na koních, král s služebníky svými i s lidem svým.
Gama in ka lura da bin waɗannan umarnai, to, sarakunan da suke zaune a gadon sarautar Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan fada, suna hawan kekunan yaƙi da dawakai, fadawansu da mutanensu suna musu rakiya.
5 Jestliže pak neuposlechnete slov těchto, skrze sebe přisahám, dí Hospodin, že poušť bude dům tento.
Amma in ba ku kiyaye waɗannan umarnai ba, in ji Ubangiji, na rantse da kaina cewa wannan fada za tă zama kufai.’”
6 Nebo takto praví Hospodin o domu krále Judského: Byl jsi mi jako Galád a vrch Libánský, ale obrátím tě jistotně v poušť jako města, v nichž se bydliti nemůže.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da wannan fadar sarkin Yahuda, “Ko da yake kina kamar Gileyad a gare ni, kamar ƙwanƙolin Lebanon, tabbatacce zan maishe ki hamada, kamar garuruwan da ba mazauna.
7 A přistrojím na tebe zhoubce, jednoho každého se zbrojí jeho, kteřížto zpodtínají nejvýbornější cedry tvé, a vmecí na oheň.
Zan aika da mai hallakarwa a kanki, kowane mutum da makamansa, za su kuma yayyanka gumaguman al’ul na ki masu kyau su jefa su cikin wuta.
8 A když půjdou národové mnozí mimo město toto, a řekne jeden druhému: Proč tak učinil Hospodin městu tomuto velikému?
“Mutane daga al’ummai da yawa za su ratsa cikin wannan birni su kuma tambayi juna suna cewa, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi haka da wannan babban birni?’
9 Tedy řeknou: Proto že opustili smlouvu Hospodina Boha svého, a klaněli se bohům cizím a sloužili jim.
Amsar kuwa za tă zama, ‘Domin sun keta alkawarin Ubangiji Allahnsu, suka yi sujada suka kuma bauta wa waɗansu alloli.’”
10 Neplačtež mrtvého, aniž ho litujte, ale ustavičně plačte příčinou toho, kterýž odchází; neboť se nenavrátí více, aby pohleděl na zemi, v níž se narodil.
Kada ku yi kuka domin sarkin da ya mutu ko ku yi makoki saboda rashinsa; a maimako, ku yi kuka mai zafi saboda wanda aka kai zaman bauta, domin ba zai ƙara dawowa ba ko ya ƙara ganin ƙasarsa ta haihuwa.
11 Nebo takto praví Hospodin o Sallumovi synu Joziáše, krále Judského, kterýž kraluje místo Joziáše otce svého: Když vyjde z místa tohoto, nenavrátí se sem více.
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shallum ɗan Yosiya, wanda ya gāji mahaifinsa a matsayin sarkin Yahuda amma bai bar wurin nan ba, “Ba zai ƙara dawowa ba.
12 Ale tam v tom místě, kamž jej zastěhují, umře, a tak země této neuzří více.
Zai mutu a inda suka kai shi zaman bauta; ba zai ƙara ganin wannan ƙasa ba.”
13 Běda tomu, kdož staví dům svůj s útiskem, a paláce své s křivdou, kterýž bližního svého v službu podrobuje darmo, mzdy pak jeho nedává jemu;
“Kaiton wanda ya gina gidansa ta hanyar rashin adalci, ɗakunansa na sama kuma ta hanyar rashin gaskiya, yana sa mutanen ƙasarsa suna aiki a banza ba ya biyansu wahalarsu.
14 Kterýž říká: Vystavím sobě dům veliký a paláce prostranné, kterýž prolamuje sobě okna, a tafluje cedrovím, a maluje barvou.
Yana cewa, ‘Zan gina wa kaina babban fada da manyan ɗakuna.’ Ta haka sai ya yi musu manyan tagogi ya manne musu al’ul ya yi musu ado kuma da ruwan ja.
15 Zdaliž kralovati budeš, že se pleteš v to cedrové stavení? Otec tvůj zdaliž nejídal a nepíjel? Když konal soud a spravedlnost, tedy dobře bylo jemu.
“Wannan zai mai da kai sarki ne in kana da al’ul a kai a kai? Mahaifinka bai kasance da abinci da abin sha ba? Ya yi abin da yake gaskiya da kuma daidai saboda haka kome ya kasance da lafiya da shi.
16 Když soudíval při chudého a nuzného, tedy dobře bylo. Zdaliž mně to není známé? dí Hospodin.
Ya kāre muradin matalauta da mabukata, ta haka kome ya tafi masa daidai. Ba abin da ake nufi da ba san ni ke nan ba?” In ji Ubangiji.
17 Ale oči tvé i srdce tvé nehledí než lakomství tvého, a abys krev nevinnou proléval, a nátisk a křivdu činil.
“Amma idanunka da zuciyarka sun kahu kawai a kan ƙazamar riba, da a kan zub da jinin marar laifi da kuma a kan danniya da zalunci.”
18 Protož takto praví Hospodin o Joakimovi synu Joziáše, krále Judského: Nebudouť ho kvíliti: Ach, bratře můj, aneb ach, sestro. Nebudou ho kvíliti: Ach, pane, aneb ach, kdež důstojnost jeho?
Saboda haka ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, “Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, ɗan’uwana! Kaito,’yar’uwata!’ Ba za su yi kuka dominsa ba, ‘Kaito, maigidana! Kaito, darajarsa!’
19 Pohřbem osličím pohřben bude, vyvlečen a vyvržen jsa za brány Jeruzalémské.
Za a binne shi kamar jaki za a ja shi a ƙasa a jefar a bayan ƙofofin Urushalima.”
20 Vstup na Libán a křič, i na hoře Bázan vydej hlas svůj; křič také přes brody, když potříni budou všickni milovníci tvoji.
“Ka haura zuwa Lebanon ka yi kuka, bari a ji muryarka a Bashan, yi kuka daga Abarim, gama an murƙushe dukan abokanka.
21 Mluvíval jsem s tebou v největším štěstí tvém, říkávalas: Nebuduť poslouchati. Tať jest cesta tvá od dětinství tvého; neuposlechlas zajisté hlasu mého.
Na ja maka kunne sa’ad da kake zama lafiya, amma sai ka ce, ‘Ba zan saurara ba!’ Wannan halinka ne tun kana matashi; ba ka yi mini biyayya ba.
22 Všecky pastýře tvé zpase vítr, a milovníci tvoji v zajetí půjdou. Tehdáž jistě hanbiti a styděti se budeš za všelikou nešlechetnost svou.
Iska za tă koro dukan makiyayanka abokanka kuma za su tafi zaman bauta. Sa’an nan za ka sha kunya a kuma walaƙanta ka saboda dukan muguntarka.
23 Ó ty, kteráž jsi usadila se na Libánu, jenž se hnízdíš na cedroví, jak milostná budeš, když na tě přijdou svírání a bolest jako rodičky!
Kai da kake zama a ‘Lebanon,’ kai da kake sheƙa a gine-ginen al’ul za ka yi nishi sa’ad da zafi ya auka maka, zafi kamar na mace mai naƙuda!
24 Živť jsem já, dí Hospodin, že byť pak byl Koniáš syn Joakima, krále Judského, prstenem pečetním na mé ruce pravé, však tě i odtud strhnu.
“Muddin ina raye,” in ji Ubangiji, “ko kai, Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda, ka zama zoben hatimin dama a hannuna na dama, zan kwaɓe ka.
25 A vydám tě v ruku těch, kteříž hledají bezživotí tvého, a v ruku těch, jejichž ty se oblíčeje lekáš, totiž v ruku Nabuchodonozora krále Babylonského, a v ruku Kaldejských.
Zan ba da kai ga waɗanda suke neman ranka, waɗanda kake tsoro, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga Babiloniyawa.
26 A hodím tebou i matkou tvou, kteráž tě porodila, do země cizí, tam, kdež jste se nezrodili, a tam zemřete.
Zan jefar da kai da mahaifiyar da ta haife ka zuwa wata ƙasa, inda babu ɗayanku da aka haifa a wurin, a can kuma za ka mutu.
27 Do země pak, po níž toužiti budete, abyste se navrátili tam, tam se nenavrátíte.
Ba za ka ƙara dawo ƙasar da kake marmarin dawowa ba.”
28 Zdaliž modlou ničemnou, kteráž roztřískána bývá, bude muž tento Koniáš? Zdali nádobou, v níž není žádné líbosti? Proč by vyházíni byli on i símě jeho, a uvrženi do země, o níž nevědí?
Wannan mutum Yehohiyacin ne da aka rena, fasasshen tukunya, abin da babu wanda yake so? Me ya sa za a jefar da shi da’ya’yansa a jefar da su a ƙasar da ba su sani ba?
29 Ó země, země, země, slyš slovo Hospodinovo.
Ya ke ƙasa, ƙasa, ƙasa, ki ji maganar Ubangiji!
30 Takto praví Hospodin: Zapište to, že muž tento bez dětí bude, a že se jemu nepovede šťastně za dnů jeho. Anobrž nepovede se šťastně i tomu muži, kterýž by z semene jeho seděl na stolici Davidově, a panoval ještě nad Judou.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Ka rabu da wannan mutum sai ka ce marar’ya’ya, mutumin da ba zai yi nasara a rayuwarsa ba, gama babu zuriyarsa da za tă yi nasara babu wani da zai zauna a kursiyin Dawuda ko ya ƙara yin mulkin Yahuda.”

< Jeremiáš 22 >