< Izaiáš 48 >

1 Slyštež to, dome Jákobův, kteříž se nazýváte jménem Izraelovým, a z vod Judových jste pošli, kteříž přisaháte ve jménu Hospodinovu, a Boha Izraelského připomínáte, však ne v pravdě, ani v spravedlnosti,
“Ku kasa kunne ga wannan, ya gidan Yaƙub, waɗanda ake kira da sunan Isra’ila suka kuma fito daga zuriyar Yahuda, ku da kuke yin rantsuwa da sunan Ubangiji kuna kuma kira sunan Allah na Isra’ila, amma ba da gaskiya ko adalci ba,
2 Ačkoli od města svatého se jmenujete, a na Boha Izraelského, jehož jméno jest Hospodin zástupů, zpoléháte.
ku da kuke kiran kanku’yan ƙasar birni mai tsarki kuna kuma dogara ga Allah na Isra’ila, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa,
3 Předešlé věci zdávna jsem oznamoval, a což vyšlo z úst mých, i což jsem ohlašoval, brzce jsem činíval, a stávalo se.
na nanata abubuwan da suka riga suka faru tuntuni, bakina ya yi shelar su na kuma sanar da su; sai nan da nan na aikata, suka kuma faru.
4 Věděl jsem, že jsi zatvrdilý, a houžev železná šíje tvá, a čelo tvé ocelivé.
Gama na san yadda kuke da taurinkai; jijiyoyin wuyanku ƙarafa ne, goshinku tagulla ne.
5 A protožť jsem oznamoval z dávna, prvé než přicházelo, ohlašovalť jsem, abys neříkal: Modla má učinila ty věci, a rytina má neb slitina má přikázala to.
Saboda haka na faɗa waɗannan abubuwa tuntuni; kafin su faru na yi shelarsu gare ku saboda kada ku ce, ‘Gumakana ne suka yi su; siffar itacena da allahn zinariyana ne ya ƙaddara su.’
6 Slýchals o tom, pohlediž na to na všecko, vy pak, nebudete-liž toho oznamovati? Již nyní ohlašujiť nové a tajné věci, o nichž jsi ty nic nevěděl.
Kun riga kun ji waɗannan abubuwa; kuka gan su duka. Ba za ku yarda da su ba? “Daga yanzu zuwa gaba zan faɗa muku sababbin abubuwa, na ɓoyayyun abubuwan da ba ku sani ba.
7 Nyní stvořeny jsou, a ne předešlého času, o nichž jsi před tímto dnem nic neslyšel, abys neřekl: Aj, věděl jsem o tom.
Yanzu an halicce su, ba da daɗewa ba; ba ku riga kun ji game da su kafin yau ba. Saboda haka ba za ku ce, ‘I, na san da su ba.’
8 Anobrž aniž jsi slyšel, ani věděl, aniž se to tehdáž doneslo ucha tvého; nebo jsem věděl, že sobě velmi nevážně počínati budeš, a že jsi převrácenec hned od života matky.
Ba ku ji ko balle ku gane ba; tun da kunnenku bai buɗu ba. Tabbatacce na san yadda kun zama masu tayarwa; an kira ku’yan tawaye daga haihuwa.
9 Pro jméno své poshovím s prchlivostí svou, a pro chválu svou poukrotím hněvu proti tobě, abych tě nevyplénil.
Saboda girman sunana na jinkirta fushina; saboda girman yabona na janye shi daga gare ku, don dai kada a yanke ku.
10 Aj, přepálím tě, ačkoli ne jako stříbro, přeberu tě v peci ssoužení.
Duba, na tace ku, ko da yake ba kamar azurfa ba; na gwada ku cikin wutar wahala.
11 Pro sebe, pro sebe učiním to. Nebo jakž by mohlo v lehkost vydáno býti? Slávy své zajisté jinému nedám.
Saboda girmana, saboda girmana, na yi haka. Yaya zan ƙyale a ƙazantar da kaina? Ba zan raba ɗaukakata da wani ba.
12 Slyš mne, Jákobe a Izraeli, povolaný můj: Já jsem, já první, já jsem i poslední.
“Ka kasa kunne gare ni, ya Yaƙub, Isra’ila, wanda na kira cewa, Ni ne shi; ni ne na farko ni ne kuma na ƙarshe.
13 Má zajisté ruka založila zemi, a pravice má dlaní rozměřila nebesa; povolal jsem jich, a hned se postavily.
Hannuna ne ya kafa harsashen duniya, hannuna na dama kuma ya shimfiɗa sammai; sa’ad da na kira su, duka suka miƙe tsaye gaba ɗaya.
14 Shromažďte se vy všickni, a slyšte. Kdo z nich oznámil tyto věci: Hospodin miluje jej, onť vykoná vůli jeho proti Babylonu, a rámě jeho proti Kaldejským?
“Ku tattaru, dukanku ku kuma saurara, Wanne a cikin gumakan ya iya faɗa waɗannan abubuwa? Zaɓaɓɓen da Ubangiji yake ƙauna zai aikata nufinsa a kan Babilon; hannunsa zai yi gāba da Babiloniyawa.
15 Já, já mluvil jsem, protož povolám ho; přivedu jej, a šťastnou bude míti cestu svou.
Ni kaina, na faɗa; I, na kira shi. Zan kawo shi, zai kuma yi nasara a cikin aikinsa.
16 Přistupte ke mně, slyšte to: Nemluvíval jsem z počátku v skrytě; od toho času, v kterémž se to dálo, přítomen jsem byl. A nyní Panovník Hospodin poslal mne a duch jeho.
“Ku zo kusa da ni ku kuma saurari wannan. “Daga farkon shela ban yi magana a ɓoye ba; a lokacin da ya faru, ina nan a wurin.” Yanzu kuwa Ubangiji Mai Iko Duka ya aiko ni, da Ruhunsa.
17 Toto praví Hospodin vykupitel tvůj, Svatý Izraelský: Já Hospodin Bůh tvůj učím tě, abys prospěch bral, a vodím tě po cestě, po kteréž bys chodil.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, Mai Fansarku, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya ce, “Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya koya muku abin da ya fi muku kyau, wanda ya muku hanyar da za ku bi.
18 Ó kdybys byl šetřil přikázaní mých, bylť by jako potok pokoj tvůj, a spravedlnost tvá jako vlny mořské.
Da a ce kawai za ku mai da hankali ga umarnaina, da salamarku ta zama kamar kogi, adalcinku kamar raƙuman teku.
19 A bylo by jako písku semene tvého, a plodu života tvého jako štěrku jeho, aniž by vyťato, ani vyhlazeno bylo jméno jeho před oblíčejem mým.
Da zuriyarku ta zama kamar yashi,’ya’yanku kamar tsabar hatsin da ba a iya ƙidayawa; da ba za a taɓa yanke sunansu balle a hallaka su daga gabana ba.”
20 Vyjděte z Babylona, utecte od Kaldejských, hlasem zvučným zvěstujte, ohlašujte to, rozneste to až do končin země. Rcete: Vykoupil Hospodin služebníka svého Jákoba.
Ku bar Babilon, ku gudu daga Babiloniyawa! Ku yi shelar wannan da sowa ta farin ciki ku kuma furta shi. Ku aika shi zuwa iyakokin duniya; ku ce, “Ubangiji ya fanshi bawansa Yaƙub.”
21 Nebudouť žízniti, když je po pustinách povede, vody z skály vyvede jim; nebo rozetne skálu, aby tekly vody.
Ba su ji ƙishi ba sa’ad da ya bishe su a cikin hamada; ya sa ruwa ya malalo dominsu daga dutse; ya tsage dutse ruwa kuwa ya kwararo.
22 Nemajíť žádného pokoje, praví Hospodin, bezbožní.
“Babu salama ga mugaye” in ji Ubangiji.

< Izaiáš 48 >