< Hozeáš 1 >
1 Slovo Hospodinovo, kteréž se stalo k Ozeášovi synu Bérovu za dnů Uziáše, Jotama, Achasa, Ezechiáše, králů Judských, a za dnů Jeroboáma syna Joasova, krále Izraelského.
Maganar Ubangiji da ta zo wa Hosiya ɗan Beyeri a zamanin mulkin Uzziya, Yotam, Ahaz da Hezekiya, sarakunan Yahuda, da zamanin mulkin Yerobowam ɗan Yowash sarkin Isra’ila.
2 Když Hospodin začal mluviti k Ozeášovi, řekl Hospodin Ozeášovi: Jdi, pojmi sobě ženu smilnou, a děti z smilstva; nebo nestydatě smilněci tato země, odvrátila se od Hospodina.
Sa’ad da Ubangiji ya fara magana ta wurin Hosiya, Ubangiji ya ce masa, “Ka tafi, ka auro wa kanka mazinaciya da’ya’yan da aka haifa ta hanyar rashin aminci, domin ƙasar tana da laifin mummunan zina ta wurin rabuwa da Ubangiji.”
3 A tak šel a pojal Gomeru, dceru Diblaimskou, kterážto počala a porodila jemu syna.
Saboda haka sai ya auri Gomer’yar Dibilayim, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa namiji.
4 Tedy řekl jemu Hospodin: Nazoviž jméno jeho Jezreel; nebo po malém času já vyhledávati budu krve Jezreel na domu Jéhu, a přestati káži království domu toho.
Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba shi suna Yezireyel, domin ba da daɗewa ba zan hukunta gidan Yehu saboda kisan da aka yi a Yezireyel, zan kuma kawo ƙarshen mulkin Isra’ila.
5 I stane se v ten den, že polámi lučiště Izraelovo v údolí Jezreel.
A wannan rana zan karye ƙarfin Isra’ila a Kwarin Yezireyel.”
6 Opět počala znovu a porodila dceru. I řekl jemu: Nazov jméno její Lorucháma; nebo již více neslituji se nad domem Izraelským, abych jim co prominouti měl.
Gomer ta sāke ɗauki ciki ta kuma haifi’ya mace. Sai Ubangiji ya ce wa Hosiya, “Ka ba ta suna, Lo-Ruhama, gama ba zan ƙara nuna wa gidan Isra’ila ƙauna ba, har da zan gafarta musu.
7 Ale nad domem Judským se slituji, a vysvobodím je skrze Hospodina Boha jejich; nebo nevysvobodím jich lučištěm a mečem, ani bojem, koňmi neb jezdci.
Duk da haka zan nuna ƙauna ga gidan Yahuda; zan kuma cece su, ba da baka, takobi ko yaƙi ba, ko ta wurin dawakai, ko masu hawan dawakai ba, sai ko ta wurin Ubangiji Allahnsu.”
8 Potom ostavivši Loruchámu, opět počala a porodila syna.
Bayan ta yaye Lo-Ruhama, sai Gomer ta sāke haifi wani ɗa namiji.
9 I řekl: Nazov jméno jeho Loammi; nebo vy nejste lid můj, a já také nebudu váš.
Sai Ubangiji ya ce, “Ka ba shi suna Lo-Ammi, gama ku ba mutanena ba ne, ni kuma ba Allahnku ba ne.
10 A však bude počet synů Izraelských jako písku mořského, kterýž ani změřen, ani sečten býti nemůže. A stane se, že místo toho, kdež řečeno jim bylo: Nejste vy lid můj, řečeno jim bude: Synové Boha silného a živého jste.
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
11 I budou shromážděni synové Judští a synové Izraelští spolu, a ustanovíce nad sebou hlavu jednu, vyjdou z této země, ačkoli veliký bude den Jezreel.
Mutanen Yahuda da mutanen Isra’ila za su sāke haɗu su zama ɗaya, za su kuma naɗa shugaba guda su kuma fita daga ƙasar, gama ranar za tă zama mai girma wa Yezireyel.