< 1 Mojžišova 16 >

1 Sarai pak manželka Abramova jemu nerodila; a měla děvku Egyptskou, jménem Agar.
To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
2 I řekla Sarai Abramovi: Aj, nyní Hospodin zavřel život můj, abych nerodila; vejdi, prosím, k děvce mé, zda bych aspoň z ní mohla míti syny. I povolil Abram řeči Sarai.
saboda haka sai ta ce wa Abram, “Ubangiji ya hana mini haihuwar’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
3 Tedy vzavši Sarai manželka Abramova Agar Egyptskou děvku svou, po desíti letech, jakž bydliti počal Abram v zemi Kananejské, dala ji Abramovi muži svému za ženu.
Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
4 I všel k Agar, kterážto počala. Viduci pak ona, že počala, zlehčila sobě paní svou.
Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
5 I řekla Sarai Abramovi: Křivdou mou tys vinen; já jsem dala děvku svou v lůno tvé, kterážto viduci, že počala, zlehčila mne sobě. Sudiž Hospodin mezi mnou a mezi tebou.
Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
6 I řekl Abram k Sarai: Aj, děvka tvá v moci tvé; učiň s ní, cožť se za dobré vidí. Tedy trápila ji Sarai, a ona utekla od ní.
Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
7 Našel ji pak anděl Hospodinův u studnice vody na poušti, u studnice té, kteráž jest při cestě Sur.
Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
8 A řekl: Agar, děvko Sarai, odkud jdeš, a kam se béřeš? I řekla: Od tváři Sarai paní své já utíkám.
Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
9 Tedy řekl jí anděl Hospodinův: Navrať se ku paní své, a pokoř se pod ruku její.
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
10 Opět řekl anděl Hospodinův: Velice rozmnožím símě tvé, aniž bude moci sečteno býti pro množství.
Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
11 Potom také řekl anděl Hospodinův: Aj, ty jsi těhotná, a tudíž porodíš syna, a nazůveš jméno jeho Izmael; nebo uslyšel Hospodin trápení tvé.
Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
12 Budeť pak lítý člověk; ruce jeho proti všechněm, a ruce všech proti němu; a před tváří všech bratří svých bydliti bude.
Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan’yan’uwansa.”
13 I nazvala Agar jméno Hospodinovo, kterýž mluvil jí: Ty jsi silný Bůh vidění; nebo řekla: Zdaliž teď také nevidím po tom, kterýž mne viděl?
Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
14 Protož nazvala studnici tu studnicí Živého vidoucího mne. Aj, ta jest mezi Kádes a Barad.
Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
15 Porodila pak Agar Abramovi syna; a nazval Abram jméno syna svého, kteréhož porodila Agar, Izmael.
Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
16 Abram pak byl v osmdesáti šesti letech, když mu porodila Agar Izmaele.
Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.

< 1 Mojžišova 16 >