< Galatským 1 >
1 Pavel apoštol, (ne od lidí, ani skrze člověka, ale skrze Jezukrista, a Boha Otce, kterýž jej vzkřísil z mrtvých, )
Bulus manzo, aikakke ba daga wurin mutum ba, ba kuma ta wurin mutane ba, amma ta wurin Yesu Kiristi da kuma Allah Uba, wanda ya tā da Yesu daga matattu.
2 I ti, kteříž se mnou jsou, všickni bratří zborům Galatským:
Dukan’yan’uwan kuma da suke tare da ni a nan, Suna gai da ikkilisiyoyi a Galatiya.
3 Milost vám a pokoj od Boha Otce a Pána našeho Jezukrista,
Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
4 Kterýž vydal sebe samého za hříchy naše, aby nás vytrhl z tohoto přítomného věku zlého, podlé vůle Boha a Otce našeho, (aiōn )
Shi wanda ya ba da kansa saboda zunubanmu don yă cece mu daga wannan mugun zamani na yanzu, bisa ga nufin Allah wanda yake kuma Ubanmu, (aiōn )
5 Jemuž buď sláva na věky věků. Amen. (aiōn )
a gare shi ɗaukaka ta tabbata har abada abadin. Amin. (aiōn )
6 Divím se, že jste tak rychle od toho, kterýž vás povolal v milost Kristovu, uchýlili se k jinému evangelium.
Ina mamaki yadda kuka yi saurin yashe wanda ya kira ku ta wurin alherin Kiristi, kuna juyewa ga wata bishara dabam
7 Kteréž není jiné, ale jsou někteří, ješto vás kormoutí, a převrátiti chtějí evangelium Kristovo.
wadda a gaskiya ba bishara ba ce ko kaɗan. Tabbatacce waɗansu mutane suna birkitar da ku, suna kuma ƙoƙari su karkatar da bisharar Kiristi.
8 Ale bychom pak i my neb anděl s nebe kázal vám mimo to, což jsme vám kázali, prokletý buď.
Amma ko mu, ko mala’ika daga sama ya yi wa’azin wata bishara dabam da wadda muka yi muku, bari yă zama la’ananne har abada!
9 Jakož jsme prvé pověděli, a ještě znovu pravím: Jestliže by vám kdo jiné evangelium kázal mimo to, kteréž jste přijali, prokletý buď.
Kamar yadda muka riga muka faɗa, haka yanzu ma ina ƙara cewa in wani yana muku wa’azin wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, bari yă zama la’ananne har abada!
10 Nebo lidské-liž věci, čili Boží předkládám? Zdaliž lidem se líbiti hledám? Kdybych se zajisté ještě lidem zaliboval, služebník Kristův bych nebyl.
Za a ce, ina ƙoƙarin neman amincewar mutane ne, ko amincewa ta Allah? Ko kuwa ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne? Da a ce har yanzu ina ƙoƙarin faranta wa mutane zuciya ne, ai, da ban zama bawan Kiristi ba.
11 Oznamujiť pak vám, bratří, že evangelium to, kteréž kázáno jest ode mne, není podlé člověka.
Ina so ku sani’yan’uwa, cewa bisharar da nake wa’azi, ba mutum ne ya ƙago ta ba.
12 Nebo aniž jsem já ho přijal od člověka, ani se naučil, ale skrze zjevení Ježíše Krista.
Ban karɓe ta daga wurin wani mutum ba, ba a kuma koya mini ita ba, a maimako, na karɓe ta, ta wurin wahayi daga Yesu Kiristi ne.
13 Slýchali jste zajisté o mém obcování někdejším v Židovstvu, že jsem se převelice protivil církvi Boží, a hubil jsem ji,
Kun dai ji labarin rayuwata ta dā a cikin Yahudanci, yadda na tsananta wa ikkilisiyar Allah ƙwarai, na kuma yi ƙoƙarin hallaka ta.
14 A že jsem prospíval v Židovstvu nad mnohé mně rovné v pokolení svém, byv velmi horlivý milovník otcovských ustanovení.
Na ci gaba a cikin Yahudanci fiye da yawancin Yahudawan da suke tsarana, na kuma yi ƙwazo ƙwarai ga bin al’adun kakannina.
15 Ale když se zalíbilo Bohu, kterýž mne byl oddělil z života matky mé, a povolal skrze milost svou,
Amma sa’ad da Allah, wanda ya keɓe ni daga mahaifa ya kira ni ta wurin alherinsa, ya kuma gamshe shi
16 Zjeviti Syna svého mně, abych jej kázal mezi pohany, hned jsem se neporadil s tělem a krví;
yă bayyana Ɗansa a cikina, domin in yi wa’azinsa cikin Al’ummai. Ban nemi shawarar wani mutum ba.
17 Aniž jsem se vrátil do Jeruzaléma k těm, kteříž prvé byli apoštolé nežli já, ale šel jsem do Arabie, přišel jsem pak zase do Damašku.
Ban kuma tafi Urushalima domin in ga waɗanda suka riga ni zaman manzanni ba, sai dai na hanzarta na tafi ƙasar Arabiya, daga baya sai na koma Damaskus.
18 Potom po třech letech navrátil jsem se do Jeruzaléma, abych navštívil Petra, a pobyl jsem u něho patnácte dní.
Bayan shekara uku, sai na haura zuwa Urushalima domin in sadu da Bitrus, na kuwa zauna tare da shi kwana goma sha biyar.
19 Jiného pak z apoštolů žádného jsem neviděl než Jakuba, bratra Páně.
Ban ga wani a ciki sauran manzanni ba, sai dai Yaƙub ɗan’uwan Ubangiji.
20 Cožť pak píši vám, aj, před Bohem, žeť neklamám.
Ina tabbatar muku a gaban Allah cewa abin da nake rubuta muku ba ƙarya ba ne.
21 Potom přišel jsem do krajin Syrských a Cilických.
Daga baya sai na tafi Suriya da Silisiya.
22 Nebyl jsem pak známý osobou zborům Židovským, kteříž byli v Kristu,
Ikkilisiyoyin da suke cikin Kiristi da suke a Yahudiya ba su san ni ba tukuna.
23 Než toliko slýchali: Že ten, kterýž se nám někdy protivil, již nyní káže víru, kterouž někdy vybojovával.
Sun dai sami labari ne kawai cewa, “Mutumin da dā yake tsananta mana yanzu yana wa’azin bangaskiyar da dā ya yi ƙoƙari yă hallaka.”
24 A slavili ve mně Boha.
Sai suka yabi Allah saboda ni.