< Ezechiel 29 >
1 Léta desátého, desátého měsíce, dvanáctého dne téhož měsíce, stalo se slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
A shekara ta goma, a wata na goma, a rana ta goma sha biyu, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Synu člověčí, obrať tvář svou proti Faraonovi králi Egyptskému, a prorokuj proti němu i proti všemu Egyptu.
“Ɗan mutum, ka fuskanci Fir’auna sarkin Masar ka kuma yi annabci gāba da shi da dukan Masar.
3 Mluv a rci: Takto praví Panovník Hospodin: Aj, já proti tobě jsem, ó Faraone králi Egyptský, draku veliký, kterýž ležíš u prostřed řek svých, ješto říkáš: Já mám řeku svou, já zajisté jsem ji přivedl sobě.
Yi masa magana ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Ina gāba da kai, Fir’auna sarkin Masar, kai babban mugun dodon ruwa kwance cikin rafuffukanka. Ka ce, “Nilu nawa ne; na yi shi wa kaina.”
4 Protož dám udici do čelistí tvých, a učiním, že zváznou ryby řek tvých na tvých šupinách; i vyvleku tě z prostředku řek tvých, i všecky ryby řek tvých na šupinách tvých zvázlé.
Amma zan sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in sa kifin rafuffukanka su manne wa kamɓorinka. Zan jawo ka daga cikin tsakiyar rafuffukanka, da dukan kifayen rafuffukanka, waɗanda suka manne a ƙamborinka,
5 A nechám tě na poušti, tebe i všech ryb řek tvých. Na svrchku pole padneš, nebudeš sebrán ani shromážděn; šelmám zemským i ptactvu nebeskému dám tě k sežrání.
Zan bar ka a cikin hamada, kai da dukan kifin rafuffukanka. Za ka fāɗi a fili ba kuwa za a tattara ka ko a kwashe ba. Zan ba da kai kamar abinci ga namun jeji na duniya da tsuntsayen sararin sama.
6 I zvědí všickni obyvatelé Egyptští, že já jsem Hospodin, proto že jste holí třtinovou domu Izraelskému.
Ta haka dukan waɗanda suke zama a Masar za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Ka zama sandan iwa domin gidan Isra’ila.
7 Když se chytají tebe rukou, lámeš se, a roztínáš jim všecko rameno; a když se na tě zpodpírají, ztroskotána býváš, ačkoli nastavuješ jim všech bedr.
Sa’ad da suka kama ka da hannuwansu, ka tsattsage, ka kuma buɗu a kafaɗunsu; sa’ad da suka jingina a kanka, sai ka karye, bayansu kuwa ya firgita.
8 Protož takto praví Panovník Hospodin: Aj, já přivedu na tě meč, a vypléním z tebe lidi i hovada.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan kawo takobi a kanka in kashe mutane da dabbobi.
9 I bude země Egyptská pustinou a pouští, i zvědí, že já jsem Hospodin, proto že říkal: Řeka má jest, já zajisté jsem ji přivedl.
Masar za tă zama kufai. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji. “‘Domin ka ce, “Nilu nawa ne; ni na yi shi,”
10 Protož aj, já budu proti tobě i proti řece tvé, a obrátím zemi Egyptskou v pustiny, v poušť přehroznou od věže Sevéne až do pomezí Mouřenínského.
saboda haka ina gāba da kai da rafuffukanka, zan kuma maishe ƙasar Masar ta lalace ta kuma zama kango daga Migdol zuwa Aswan, har iyakar Kush.
11 Nepůjdeť přes ni noha člověka, ani noha dobytčete půjde přes ni, a nebude v ní bydleno za čtyřidceti let.
Ba ƙafar mutum ko ta dabbar da za tă ratsa ta; ba wanda zai zauna a can har shekaru arba’in.
12 A tak uvedu zemi Egyptskou v pustinu nad jiné země pusté, a města její nad jiná města zpuštěná pustá budou za čtyřidceti let, když rozptýlím Egyptské mezi národy, a rozženu je do rozličných zemí.
Zan mai da ƙasar Masar kufai a cikin ƙasashen da aka ragargaza, biranenta kuma za su zama kango har shekaru arba’in a cikin biranen da aka lalace. Zan watsar da Masarawa a cikin al’ummai in warwatsa su cikin ƙasashe.
13 A však takto praví Panovník Hospodin: Po skonání čtyřidceti let shromáždím Egyptské z národů, kamž rozptýleni budou.
“‘Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ƙarshen shekaru arba’in ɗin zan tattara Masarawa daga al’ummai inda aka warwatsa su.
14 A přivedu zase zajaté Egyptské, a uvedu je zase do země Patros, do země přebývání jejich, i budou tam královstvím sníženým.
Zan komo da su daga zaman bauta in mai da su zuwa Masar ta Bisa, ƙasarsu ta ainihi. A can za su zama masarauta marar ƙarfi.
15 Mimo jiná království bude sníženější, aniž se bude vynášeti více nad jiné národy; zmenším je zajisté, aby nepanovali nad národy.
Za tă zama masarauta mafi rarrauna cikin masarautai, ba kuwa za tă ƙara ɗaga kanta a kan sauran al’ummai ba. Zan sa tă zama marar ƙarfi ƙwarai, har da ba za tă ƙara yin mulkin a kan al’ummai ba.
16 I nebude více domu Izraelskému doufáním, kteréž by na pamět přivodilo nepravost, když by se obraceli za nimi; nebo zvědí, že já jsem Panovník Hospodin.
Masar ba za tă ƙara zama abin dogara ga mutanen Isra’ila ba amma za tă zama abin tunin zunubinsu na juyawa gare ta don taimako. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Mai Iko Duka.’”
17 Potom bylo dvadcátého sedmého léta, prvního měsíce, prvního dne, že se stalo slovo Hospodinovo ke mně, řkoucí:
A shekara ta ashirin da bakwai, a wata na fari a rana ta farko, maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
18 Synu člověčí, Nabuchodonozor král Babylonský podrobil vojsko své v službu velikou proti Týru. Každá hlava oblezla, a každé rameno odříno jest, mzdy pak nemá, on ani vojsko jeho, z Týru za tu službu, kterouž sloužili proti němu.
“Ɗan mutum, Nebukadnezzar sarkin Babilon ya sa sojojinsa su matsa wa Taya; kowane kai ya koɗe, kowace kafaɗa kuma ta goge. Duk da haka shi da sojojinsa ba su sami wani lada daga matsin da suka yi a kan Taya ba.
19 Z té příčiny takto praví Panovník Hospodin: Aj, já dávám Nabuchodonozorovi králi Babylonskému zemi Egyptskou, aby pobral zboží její, a rozebral loupeže její, i rozchvátal kořisti její, aby mělo mzdu vojsko jeho.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan ba da Masar ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai washe dukiyarta. Zai kwashe ya washe ƙasar ganima a matsayin abin biyan sojojinsa.
20 Za práci jejich, kterouž mi sloužili, dám jim zemi Egyptskou, proto že mně pracovali, praví Panovník Hospodin.
Saboda haka na ba shi Masar a matsayin lada don ƙoƙarinsa domin shi da sojojinsa sun yi wannan domina ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 V ten den rozkáži vypučiti se rohu domu Izraelského. Tobě též způsobím, že otevřeš ústa u prostřed nich, i zvědí, že já jsem Hospodin.
“A wannan rana zan sa ƙaho ya tsiro wa gidan Isra’ila, zan kuma buɗe bakinka a cikinsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”