< Skutky Apoštolů 26 >
1 Potom Agrippa řekl Pavlovi: Dopouštíť se, abys sám za sebe promluvil. Tedy Pavel vztáh ruku, tuto zprávu dával:
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “An ba ka izini ka yi magana.” Saboda haka Bulus ya yi alama da hannunsa ya fara kāriyarsa.
2 Na všecky ty věci, z kterýchž mne viní Židé, králi Agrippo, za šťastného se počítám, že dnes před tebou odpovídati mám,
Ya ce, “Sarki Agiriffa, na yi sa’a da na tsaya a gabanka yau yayinda nake kāriyata game da dukan zargin Yahudawa,
3 A zvláště proto, poněvadž jsi ty povědom všech těch, kteříž u Židů jsou, obyčejů a otázek. Protož prosím tebe, vyslyšiž mne trpělivě.
musamman ma domin ka saba sosai da dukan al’adun Yahudawa da kuma maganganunsu. Saboda haka ina roƙonka ka saurare ni da haƙuri.
4 O životu mém od mladosti, jaký byl od počátku v národu mém v Jeruzalémě, vědí všickni Židé,
“Yahudawa duk sun san yadda na yi rayuwa tun ina yaro, daga farkon rayuwata a ƙasarmu da kuma a Urushalima.
5 Měvše mne prvé zdávna v dobré známosti, (kdyby chtěli svědectví vydati, ) kterak vedlé nejjistší sekty v našem náboženství byl jsem živ farizeus.
Sun san ni tun da daɗewa za su kuwa shaida, in suna so, cewa bisa ga ɗarikar addininmu mafi tsanani, na yi rayuwar Bafarisiye ne.
6 A nyní pro naději toho zaslíbení, kteréž se stalo otcům od Boha, stojím, soudu jsa poddán,
Yanzu kuwa saboda begena cikin abin da Allah ya yi wa kakanninmu alkawari ne, ake mini shari’a yau.
7 K kterémuž dvanáctero pokolení naše, sloužíce Bohu ustavičně dnem i nocí, naději má, že přijde. Pro tuť naději žalují na mne Židé, ó králi Agrippo.
Wannan shi ne alkawarin da kabilanmu goma sha biyu suke bege su ga cikawarsa, yayinda suke bauta wa Allah da himma dare da rana. Ya Sarki, saboda wannan bege ne fa Yahudawa suke zargena.
8 A tak-liž se to od vás za nepodobné k víře soudí, že Bůh křísí mrtvé?
Don me wani a cikinku zai yi shakka cewa Allah yana tā da matattu?
9 Ačť mně se zdálo, že by náležité bylo, proti jménu Ježíše Nazaretského mnoho odporného činiti,
“Ni ma a dā na tabbata cewa ya kamata in yi duk abin da zan iya yi domin in yi gāba da sunan Yesu Banazare.
10 Jakož jsem i činil v Jeruzalémě, a mnohé z svatých já jsem do žalářů dával, vzav moc od předních kněží. A když měli mordování býti, já jsem pomáhal ortele vynášeti.
Abin da na yi ke nan a Urushalima. Da izinin manyan firistoci na sa tsarkaka da yawa a kurkuku, sa’ad da kuma ake kashe su, nakan ka da ƙuri’ata gāba da su.
11 A po všech školách často je trápě, přinucoval jsem rouhati se; a náramně rozlítiv se na ně, sháněl jsem se po nich i v jiných městech.
Sau da dama nakan bi majami’a-majami’a, in sa a yi musu hukunci. Na kuma yi ƙoƙarin tilasta su su yi saɓo. Don kuma tsananin fushi da su, sai da na fafare su har waɗansu garuruwa na ƙetaren iyaka, ina tsananta musu.
12 A v tom, když jsem šel do Damašku, s mocí a s poručením předních kněží,
“A cikin irin tafiye-tafiyen nan ne ina kan hanya zuwa Damaskus tare da izini daga manyan firistoci.
13 O poledni na cestě, ó králi, uzřel jsem, ano světlo s nebe, jasnější nad blesk slunečný, obklíčilo mne, i ty, kteříž se mnou šli.
Da tsakar rana, ya sarki, sa’ad da nake kan hanya, sai na ga wani haske daga sama, fiye da hasken rana, yana haskakawa kewaye da ni da abokan tafiyata.
14 A když jsme my všickni na zem padli, slyšel jsem hlas mluvící k sobě, a řkoucí Židovským jazykem: Sauli, Sauli, proč mi se protivíš? Tvrdoť jest tobě proti ostnům se zpěčovati.
Dukanmu muka fāɗi ƙasa, na kuwa ji wata murya tana ce mini da harshen Arameyik, ‘Shawulu, Shawulu, don me kake tsananta mini? Yana da wuya ka shuri tsinken tsokanar dabba.’
15 A já jsem řekl: I kdo jsi, Pane? A on řekl: Já jsem Ježíš, kterémuž ty se protivíš.
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Ni ne Yesu wanda kake tsananta wa.
16 Ale vstaň a stůj na nohách svých; nebo protoť jsem se tobě ukázal, abych tebe učinil služebníkem a svědkem i těch věcí, kteréž jsi viděl, i těch, v kterýchž ukazovati se budu tobě,
Yanzu ka tashi, ka tsaya da ƙafafunka. Na bayyana a gare ka don in naɗa ka bawa da kuma mai shaidar abin da ka gani game da ni da kuma abin da zan nuna maka.
17 Vysvobozuje tebe z lidu tohoto, i z pohanů, k nimž tě nyní posílám,
Zan tsirar da kai daga mutanenka da kuma daga Al’ummai. Ina aikan ka zuwa gare su domin
18 Otvírati oči jejich, aby se obrátili od temností k světlu, a z moci ďábelské k Bohu, aby tak hříchů odpuštění a díl s posvěcenými vzali skrze víru, kteráž jest ve mne.
ka buɗe idanunsu su kuwa juyo daga duhu zuwa haske, daga mulkin Shaiɗan kuma zuwa wurin Allah, domin su sami gafarar zunubai da kuma matsayi a cikin waɗanda aka tsarkake ta wurin bangaskiya a cikina.’
19 A protož, ó králi Agrippo, nebyl jsem nevěřící tomu nebeskému vidění.
“Saboda haka fa, Sarki Agiriffa, ban yi rashin biyayya ga wahayin nan daga sama ba.
20 Ale nejprv těm, kteříž jsou v Damašku a v Jeruzalémě, i po vší krajině Judské i pohanům zvěstoval jsem, aby pokání činili, a obrátili se k Bohu, skutky hodné činíce pokání.
Da farko ga waɗanda suke a Damaskus, sa’an nan ga waɗanda suke a Urushalima da kuma cikin dukan Yahudiya, da kuma ga Al’ummai su ma, na yi wa’azi don su tuba su juyo ga Allah su kuma tabbatar da tubansu ta wurin ayyukansu.
21 A pro tu příčinu Židé javše mne v chrámě, pokoušeli se rukama zamordovati.
Shi ya sa Yahudawa suka kama ni a filin haikali suka kuma yi ƙoƙarin kashe ni.
22 Ale s pomocí Boží ještě až do dnešního dne stojím, vydávaje svědectví i malému i velikému, nic jiného nevypravuje, než to, což proroci a Mojžíš zvěstovali, že se mělo státi:
Amma na sami taimakon Allah har yă zuwa yau. Yanzu ga ni a tsaye a nan, ina shaida ga babba da yaro. Ba na faɗin kome fiye da abin da annabawa da Musa suka ce zai faru,
23 Že měl Kristus trpěti, a z mrtvých vstana první, zvěstovati světlo lidu tomuto i pohanům.
cewa Kiristi zai sha wahala, kuma a matsayin wanda yake na fari da zai tashi daga matattu, zai yi shelar haske ga mutanensa da kuma Al’ummai.”
24 To když od sebe promluvil Pavel, Festus hlasem velikým řekl: Blázníš, Pavle. Mnohé tvé umění k bláznovství tebe přivodí.
A nan ne fa Festus ya tsai da kāriyar Bulus. Ya yi ihu ya ce, “Bulus! Kai dai ruɗaɗɗe ne, yawan karatunka yana juya maka kai.”
25 On pak řekl: Neblázním, výborný Feste, ale slova pravdy a středmosti mluvím.
Bulus ya amsa ya ce, “Ba na hauka, ya mafifici Festus. Abin da nake faɗi gaskiya ne da kuma mai kyau.
26 Víť zajisté o těch věcech král, před kterýmž svobodně mluvím; nebo mám za to, žeť ho nic z těchto věcí tajno není, poněvadž se toto nedálo pokoutně.
Sarki ya san waɗannan abubuwa, ina kuma iya yin magana da shi a sake. Na tabbata cewa ba ɗaya daga cikin waɗannan da ya kuɓuce saninsa, domin ba a ɓoye aka yi shi ba.
27 Věříš-li, králi Agrippo, prorokům? Vím, že věříš.
Sarki Agiriffa ka gaskata da annabawa? Na san ka gaskata.”
28 Tedy Agrippa řekl Pavlovi: Téměř bys mne k tomu naklonil, abych byl křesťanem.
Sai Agiriffa ya ce wa Bulus, “Kana tsammani cewa a cikin ɗan ƙanƙanin lokaci kana so ka mai da ni Kirista?”
29 A Pavel řekl: Žádalť bych od Boha, abyste i poněkud i z cela, netoliko ty, ale všickni, kteříž slyší mne dnes, byli takoví, jakýž já jsem, kromě okovů těchto.
Bulus ya amsa ya ce, “Ko a ɗan lokaci, ko a lokaci mai yawa, ina addu’a ga Allah cewa, ba kai kaɗai ba amma duk waɗanda suke saurare ni a yau su zama abin da nake, sai dai ban da sarƙoƙin nan.”
30 A když to Pavel promluvil, vstal král i vládař a Bernice, i ti, kteříž s nimi seděli.
Sai sarki ya tashi, haka kuma gwamna da Bernis da kuma waɗanda suke zaune tare da su.
31 A odšedše na stranu, mluvili spolu, řkouce: Nic hodného smrti neb vězení nečiní člověk tento.
Suka bar ɗakin, kuma yayinda suke magana da juna, sai suka ce, “Wannan mutum ba ya yin kome da ya isa kisa ko dauri.”
32 Agrippa pak Festovi řekl: Mohl propuštěn býti člověk tento, kdyby se byl neodvolal k císaři.
Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Da ba don wannan mutum ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar ba da an sake shi.”