< Skutky Apoštolů 20 >
1 Když pak přestala ta bouřka, povolav Pavel učedlníků, a požehnav jich, vyšel odtud, aby se bral do Macedonie.
Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
2 A když prošel ty krajiny, a napomenutí jim učiniv mnohými řečmi, přišel do země Řecké.
Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
3 A pobyv tam za tři měsíce, (kdež Židé učinili jemu zálohy, ) když se měl plaviti do Syrie, umínil navrátiti se skrze Macedonii.
inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
4 I šel s ním Sópater Berienský až do Azie, a z Tessalonicenských Aristarchus a Sekundus a Gáius Derbeus a Timoteus, z Azianských pak Tychikus a Trofimus.
Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
5 Ti šedše napřed, dočkali nás v Troadě.
Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
6 My pak plavili jsme se po velikonoci z Filippis, a přišli jsme k nim do Troady v pěti dnech, a tu jsme pobyli za sedm dní.
Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
7 Tedy první den po sobotě, když se učedlníci sešli k lámání chleba, Pavel mluvil k nim, maje nazejtří jíti pryč, i prodlil řečí až do půlnoci.
A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
8 A bylo mnoho světel na té síni, kdež byli shromážděni.
Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
9 Jeden pak mládenec, jménem Eutychus, sedě na okně, jsa obtížen hlubokým snem, když tak dlouho Pavel kázal, spě, spadl s třetího ponebí dolů a vzat jest mrtvý.
Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
10 I sstoupiv dolů Pavel, zpolehl na něj, a objav jej, řekl: Nermuťtež se, však duše jeho v něm jest.
Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
11 A vstoupiv, lámal chléb a jedl, a kázaní jim učiniv dlouho až do svitání, tak odšel pryč.
Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
12 I přivedli toho mládence živého, a byli velice potěšeni.
Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
13 My pak vstoupivše na lodí, plavili jsme se do Asson, odtud majíce k sobě vzíti Pavla; nebo byl tak poručil, maje sám jíti po zemi.
Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
14 A když se k nám připojil v Asson, vzavše jej, přijeli jsme do Mitylénu.
Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
15 A odtud plavíce se, druhý den byli jsme proti Chium, a třetího dne připlavili jsme se k Sámu, a pobyvše v Trogyllí, nazejtří přišli jsme do Milétu.
Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
16 Nebo Pavel byl umínil pominouti Efez, aby se nemeškal v Azii; nebo pospíchal, by možné jemu bylo, aby byl o letnicích v Jeruzalémě.
Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
17 Tedy z Milétu poslav do Efezu, povolal k sobě starších církve.
Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
18 Kteříž když přišli k němu, řekl jim: Vy víte od prvního dne, v kterýž přišel jsem do Azie, kterak jsem po všecken ten čas s vámi byl,
Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
19 Slouže Pánu se vší pokorou i s mnohými slzami a pokušeními, kteráž na mne přicházela z úkladů Židovských,
Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
20 Kterak jsem ničeho nepominul, což by užitečného bylo, abych vám neoznámil, a neučil vás vůbec zjevně i po domích,
Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
21 Svědectví vydávaje i Židům i Řekům o pokání k Bohu, a o víře v Pána našeho Ježíše Krista.
Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
22 A aj, nyní já sevřín jsa duchem, beru se do Jeruzaléma, nevěda, co mi se v něm má státi,
“Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
23 Než že Duch svatý po městech osvědčuje mi, pravě, že vězení a ssoužení mne očekávají.
Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
24 Však já nic na to nedbám, aniž jest mi tak drahá duše má, jen abych běh svůj s radostí vykonal, a přisluhování, kteréž jsem přijal od Pána Ježíše, k osvědčování evangelium milosti Boží.
Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
25 A aj, já nyní vím, že již více neuzříte tváři mé vy všickni, mezi kterýmiž jsem chodil, káže o království Božím.
“Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
26 Protož osvědčujiť vám v dnešní den, žeť jsem čist od krve všech.
Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
27 Nebo jsem neobmeškal zvěstovati vám všeliké rady Boží.
Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
28 Buďtež tedy sebe pilni i všeho stáda, v němž Duch svatý ustanovil vás biskupy, abyste pásli církev Boží, kteréž sobě dobyl svou vlastní krví.
Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
29 Nebo já to vím, že po mém odjití vejdou mezi vás vlci hltaví, kteříž nebudou odpouštěti stádu.
Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
30 A z vás samých povstanou muži, kteříž budou mluviti převrácené věci, aby obrátili učedlníky po sobě.
Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
31 Protož bděte, v paměti majíce, že jsem po tři léta nepřestával dnem i nocí s pláčem napomínati jednoho každého.
Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
32 A již nyní, bratří, poroučím vás Bohu a slovu milosti jeho, kterýž mocen jest vzdělati, a dáti vám dědictví mezi všemi posvěcenými.
“To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
33 Stříbra neb zlata neb roucha nežádal jsem od žádného.
Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
34 Nýbrž sami víte, že toho, čehož mi kdy potřebí bylo, i těm, kteříž jsou se mnou, dobývaly ruce tyto.
Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
35 Vše ukázal jsem vám, že tak pracujíce, musíme snášeti mdlé, a pamatovati na slova Pána Ježíše; nebť on řekl: Blahoslaveněji jest dáti nežli bráti.
Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
36 A to pověděv, klekna na kolena svá, modlil se s nimi se všemi.
Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
37 I stal se pláč veliký ode všech, a padajíce na hrdlo Pavlovo, líbali jej,
Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
38 Rmoutíce se nejvíce nad tím slovem, kteréž řekl, že by již více neměli tváři jeho viděti. I provodili jej až k lodí.
Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.