< 1 Samuelova 29 >
1 A tak shromáždili Filistinští všecka vojska svá u Afeku, Izrael pak položil se u studnice, kteráž byla v Jezreel.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 I táhla knížata Filistinská po stu a po tisících, David pak a muži jeho táhli nazad s Achisem.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 Tedy řekla knížata Filistinská: K čemu jsou Židé tito? Odpověděl Achis knížatům Filistinským: Zdaliž toto není David služebník Saule, krále Izraelského, kterýž byl při mně dnů těchto, nýbrž těchto let, a neshledal jsem na něm ničeho ode dne, jakž odpadl od Saule, až do tohoto dne?
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 I rozhněvala se na něj knížata Filistinská, a řekli jemu ta knížata Filistinská: Odešli zase muže toho, ať se navrátí k místu svému, kteréž jsi mu ukázal, a nechť netáhne s námi k boji, aby se nám nepostavil za nepřítele v bitvě. Nebo čím se zalíbiti může pánu svému tento? Zdali ne hlavami mužů těchto?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 Zdaliž tento není ten David, o kterémž zpívali v houfích plésajících, říkajíce: Porazil Saul svůj tisíc, ale David svých deset tisíců?
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 I povolal Achis Davida, a řekl jemu: Živť jest Hospodin, že jsi upřímý, a líbí mi se vycházení tvé i vcházení tvé se mnou do vojska. Nebo neshledal jsem na tobě nic zlého ode dne, v kterýž jsi přišel ke mně, až do dne tohoto, ale před očima knížat nejsi vzácný.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Protož nyní navrať se a jdi v pokoji, a nebudeš těžký v očích knížat Filistinských.
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 I řekl David Achisovi: Co jsem pak učinil, a co jsi shledal na služebníku svém ode dne, v kterýž jsem počal býti u tebe, až do tohoto dne, abych nešel a nebojoval proti nepřátelům pána svého krále?
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 A odpovídaje Achis, řekl Davidovi: Vímť, že jsi vzácný před očima mýma jako anděl Boží, ale knížata Filistinská řekla: Nechť netáhne s námi k boji.
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 Nyní tedy vstaň tím raněji a služebníci pána tvého, kteříž přišli s tebou, a vstanouce tím spíše ráno, hned jakž by zasvitávalo, odejděte.
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 I vstal David, on i muži jeho, aby odšel tím raněji, a navrátil se do země Filistinské. Filistinští pak táhli do Jezreel.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.