< 1 Samuelova 24 >
1 I stalo se, že když se navrátil Saul od honění Filistinských, oznámili jemu, řkouce: Hle, David jest na poušti Engadi.
Bayan da Shawulu ya komo daga fafaran Filistiyawa, sai aka gaya masa cewa, “Dawuda yana can a Jejin En Gedi.”
2 Tedy vzav Saul tři tisíce mužů vybraných ze všeho Izraele, odšel hledati Davida a mužů jeho na skalách kamsíků.
Saboda haka Shawulu ya zaɓi mutum dubu uku daga cikin dukan Isra’ila, suka fita neman Dawuda da mutanensa kusa da Duwatsun Awakin Jeji.
3 I přišel k stájím ovcí blízko cesty, kdež byla jeskyně, do níž všel Saul na potřebu; David pak a muži jeho seděli po stranách v té jeskyni.
Da Shawulu ya isa inda ake ajiye garken tumaki a bakin hanya inda akwai kogo, sai ya shiga ciki kogon don yă yi bayan gari. Dawuda da mutanensa kuwa suna can zaune a ƙurewar kogon.
4 Protož řekli muži Davidovi jemu: Aj, tento jest den, o němž tobě mluvil Hospodin, řka: Aj, já dám nepřítele tvého v ruku tvou, abys mu učinil, jakť se koli líbiti bude. Tedy vstav David, uřezal tiše kus pláště Saulova.
Mutanen Dawuda suka ce, wannan rana ce Ubangiji ya yi magana ya ce maka, “Zan ba da maƙiyinka a hannunka domin ka yi abin da ka ga dama da shi.” Sai Dawuda ya tashi a hankali ya je ya yanke shafin rigar Shawulu.
5 Potom pak padlo to těžce na srdce Davidovi, že uřezal křídlo pláště Saulova.
Daga baya Dawuda ya damu domin ya yanke shafin rigar Shawulu.
6 Pročež řekl mužům svým: Uchovejž mne Hospodin, abych to učiniti měl pánu mému, pomazanému Hospodinovu, abych vztáhnouti měl ruku svou na něj, poněvadž jest pomazaný Hospodinův.
Ya ce wa mutanensa, “Ubangiji yă sawwaƙe in yi abu haka ga shugabana da Ubangiji ya shafe, ko in ɗaga hannuna in kashe shi, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.”
7 A tak zabránil David mužům svým těmi slovy, a nedal jim povstati proti Saulovi. Saul také vyšed z té jeskyně, bral se cestou svou.
Da wannan magana Dawuda ya kwaɓi mutanensa, bai yarda su fāɗa wa Shawulu ba. Shawulu kuwa ya bar kogon ya yi tafiyarsa.
8 Potom vstal i David, a vyšed z jeskyně, volal za Saulem, řka: Pane můj králi! I ohlédl se Saul zpět, David pak sehnuv se tváří k zemi, poklonil se jemu.
Daga baya Dawuda ya fita daga kogon sai ya kira Shawulu ya ce, “Ranka yă daɗe, sarki!” Da Shawulu ya waiwaya, sai Dawuda ya rusuna da fuskarsa har ƙasa.
9 A řekl David Saulovi: I proč posloucháš řečí lidských, kteříž praví: Hle, David hledá tvého zlého.
Ya ce wa Shawulu, “Me ya sa kake saurari mutanen da suke cewa, ‘Dawuda ya dāge yă cuce ka’?
10 Aj, dnešního dne viděti mohly oči tvé, že tě byl vydal Hospodin dnes v ruku mou v jeskyni. A byloť mi řečeno, abych tě zabil, ale šanoval jsem tě; nebo řekl jsem: Nevztáhnuť ruky své na pána svého, poněvadž jest pomazaný Hospodinův.
Yau ka ga da idonka yadda Ubangiji ya bashe ka a hannuna a cikin kogon nan. Waɗansu sun ce mini in kashe ka, amma na bar ka, na ce, ‘Ba zan sa hannuna a kan shugabana ba, gama shi shafaffe ne na Ubangiji.’
11 Nýbrž, otče můj, pohleď a viz kus pláště svého v ruce mé, a žeť jsem nechtěl, odřezuje křídlo pláště tvého, zabiti tebe. Poznejž tedy a viz, žeť není v úmysle mém nic zlého, ani jaké převrácenosti, a žeť jsem nezhřešil proti tobě; ty pak číháš na duši mou, abys mi ji odjal.
Babana, duba, ga shafin rigarka a hannuna, na yanke shafin rigarka amma ban kashe ka ba. Yanzu ka gane ka kuma sani cewa ba ni da laifin aikata kome ko tayarwa, ban yi maka laifi ba, amma kana farautar raina.
12 Sudiž Hospodin mezi mnou a mezi tebou, a pomstiž mne Hospodin nad tebou, ale ruka má nebude proti tobě.
Ubangiji zai shari’anta tsakanina da kai. Ubangiji zai sāka mini laifin da ka yi mini, amma ni kam ba zan taɓa ka ba.
13 Jakož vzní ono přísloví starých: Od bezbožných vychází bezbožnost; protož nebudeť ruka má proti tobě.
Kamar yadda karin maganan nan na dā ya ce, ‘Daga cikin masu mugunta, mugunta ke fitowa,’ hannuna dai ba zai taɓa ka ba.
14 Na koho to jen vytáhl král Izraelský? Koho to honíš? Psa mrtvého, blechu jednu.
“Wane ne sarkin Isra’ila, ka fito kake bi? Wa kake kora? Kana bin mataccen kare ko kuɗin cizo?
15 Ale budeť Hospodin soudce; on nechť rozsoudí mezi mnou a tebou, a nechť pohledí a vyvede při mou, a vysvobodí mne z ruky tvé.
Ubangiji yă zama alƙali, yă yi shari’a tsakanina da kai, bari Ubangiji yă duba, yă tsaya mini, yă nuna ba ni da laifi.”
16 Když pak přestal David mluviti slov těch Saulovi, odpověděl Saul: Není-liž to hlas tvůj, synu můj Davide? A pozdvih Saul hlasu svého, plakal.
Da Dawuda ya gama wannan magana, sai Shawulu ya ce, “Muryarka ke nan ɗana Dawuda?” Sai ya fasa da kuka.
17 A řekl Davidovi: Spravedlivější jsi nežli já; nebo ty jsi mi odplatil se dobrým, já pak zlým tobě jsem se odplatil.
Ya ce, “Ka fi ni gaskiya, ka yi mini alheri, ni kuwa na yi maka mugunta.
18 Ty zajisté ukázal jsi dnes, že mi činíš dobře; nebo ačkoli mne byl Hospodin zavřel v ruce tvé, však jsi mne nezabil.
Ga shi yanzu ka faɗa mini alherin da ka yi mini. Ubangiji ya bashe ni a hannunka amma ba ka kashe ni ba.
19 Zdali kdo nalezna nepřítele svého, propustí ho po cestě dobré? Ale Hospodin odplatiž tobě dobrým za to, co jsi mi dnešního dne učinil.
In mutum ya sami maƙiyinsa, zai bar shi yă tafi lafiya ba tare da yin masa rauni ba? Ubangiji yă sāka maka, gama ka nuna mini alheri a yau.
20 Protož nyní, (vím, že jistotně kralovati budeš, a že stálé bude v ruce tvé království Izraelské, )
Na sani tabbatacce za ka zama sarki. Masarautar Isra’ila za tă kahu a hannunka.
21 Nyní, pravím, přisáhni mi skrze Hospodina, že nevypléníš semene mého po mně, a nevyhladíš jména mého z domu otce mého.
Yanzu ka rantse mini da Ubangiji cewa ba za ka hallaka zuriyarta ko ka share sunana daga iyalin mahaifina ba.”
22 A tak přisáhl David Saulovi. I odšel Saul do domu svého, David pak a muži jeho vstoupili na bezpečné místo.
Sai Dawuda ya rantse wa Shawulu. Sa’an nan Shawulu ya koma gida, amma Dawuda da mutanensa suka haura zuwa wurin ɓuya.