< 1 Janův 5 >
1 Každý, kdož věří, že Ježíš jest Kristus, z Boha se narodil; a každý, kdož miluje toho, kterýž zplodil, milujeť i toho, kterýž zplozen jest z něho.
Duk Wanda ya gaskata Yesu shine Almasihu haifaffe na Allah ne. Kuma duk wanda ya kaunaci uba ya kaunaci dan da uban ya haifa.
2 Po tomť poznáváme, že milujeme syny Boží, když Boha milujeme, a přikázaní jeho ostříháme.
Haka muka sani muna kaunar 'ya'yan Allah: yayin da muka kaunaci Allah, kuma muka aikata umarninsa.
3 Nebo toť je láska Boží, abychom přikázaní jeho ostříhali; a přikázaní jeho nejsou těžká.
Wannan itace kaunar Allah, cewa mu kiyaye umarninsa. Domin umarninsa ba masu nawaitawa bane.
4 Všecko zajisté, což se narodilo z Boha, přemáhá svět; a toť jest to vítězství, kteréž přemáhá svět, víra naše.
Duk wanda yake haifaffe na Allah yakan yi nasara da duniya. Wannan itace nasarar da ta rinjayi duniya, wato bangaskiyarmu.
5 Kdo jest, ješto přemáhá svět, jediné, kdož věří, že Ježíš jest Syn Boží?
Wanene wannan mai nasara da duniya? Sai dai wanda ya gaskata Yesu Dan Allah ne.
6 Toť jest ten, kterýž přišel skrze vodu a krev, Ježíš Kristus, ne u vodě toliko, ale u vodě a ve krvi. A Duch jest, kterýž svědectví vydává, že Duch jest pravda.
Wannan shine wanda yazo ta wurin ruwa da jini: Yesu Almasihu. Ya zo ba ta wurin ruwa kadai ba, amma ta wurin ruwa da jini.
7 Nebo tři jsou, kteříž svědectví vydávají na nebi: Otec, Slovo, a Duch svatý, a ti tři jedno jsou.
Domin akwai uku wadanda suke bada shaida:
8 A tři jsou, kteříž svědectví vydávají na zemi: Duch, a voda, a krev, a ti tři jedno jsou.
Ruhu, da ruwa, da kuma jini. Wadannan ukun kuwa manufarsu daya ce.
9 Poněvadž svědectví lidské přijímáme, svědectvíť Boží větší jest. Nebo totoť svědectví jest Boží, kteréž vysvědčil o Synu svém.
Idan mun karbi shaidar mutane, shaidar Allah ta fi girma. Wannan ita ce shaidar Allah, wato ya bada shaida akan Dansa.
10 Kdož věří v Syna Božího, máť svědectví sám v sobě. Kdož nevěří Bohu, lhářem jej učinil; nebo neuvěřil tomu svědectví, kteréž vysvědčil Bůh o Synu svém.
Wanda ya gaskata da Dan Allah shaidar tana nan tare da shi. Duk wanda bai bada gaskiya ga Allah ba, ya mai da shi makaryaci kenan, domin bai gaskata da shaidar da Allah ya bayar game da Dansa ba.
11 A totoť jest svědectví to, že život věčný dal nám Bůh, a ten život v Synu jeho jest. (aiōnios )
Wannan ita ce shaida: Allah ya bamu rai madawwami, wannan rai kuwa yana cikin Dansa. (aiōnios )
12 Kdožť má Syna, máť život; kdož nemá Syna Božího, života nemá.
Duk wanda yake da Dan, yana da rai. Duk wanda ba shida Dan Allah kuwa bashi da rai.
13 Tyto věci psal jsem vám věřícím ve jménu Syna Božího, abyste věděli, že máte věčný život, a abyste věřili ve jméno Syna Božího. (aiōnios )
Na rubuto maku wannan ne don ku tabbata kuna da rai madawwami—a gare ku wadanda suka gaskata da sunan Dan Allah. (aiōnios )
14 A totoť jest to smělé doufání, kteréž máme k němu, že zač bychom koli prosili podlé vůle jeho, slyší nás.
Wannan shine gabagadin da muke da shi a gabansa, wato, in mun roki kome bisa ga nufinsa, zai ji mu.
15 Že pak víme, že nás slyší, prosili-li bychom zač, podlé toho víme, že máme prosby naplněné, kteréž jsme předkládali jemu.
Haka kuma, in mun san yana jinmu—Duk abin da mu ka rokeshi—mun sani muna da duk abin da muka roka daga gare shi.
16 Viděl-li by kdo bratra svého hřešícího hříchem ne k smrti, modliž se za něj, a dá jemu Bůh život, totiž hřešícím ne k smrti. Jestiť hřích k smrti; ne za ten, pravím, aby se modlil.
Idan wani ya ga dan'uwansa ya yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba, sai yayi masa addu'a, Allah kuwa zai ba shi rai. Ina nufin wadanda suka yi zunubin da bai kai ga mutuwa ba. Akwai zunubin da yake kai wa ga mutuwa: Ban ce a yi addu'a domin wannan ba.
17 Každá nepravost jestiť hřích, ale jestiť hřích ne k smrti.
Dukkan rashin adalci, zunubi ne, amma akwai zunubin da bai kai ga mutuwa ba.
18 Víme, že každý, kdož se narodil z Boha, nehřeší; ale ten, kdož narozen jest z Boha, ostříhá sebe samého, a ten zlostník se ho nedotýká.
Mun sani kowanne haiffafe daga wurin Allah ba ya yin zunubi. Amma wanda ke haifaffe daga wurin Allah, ya kan kare shi, mugun nan kuwa ba zai iya yi masa illa ba.
19 Víme, že z Boha jsme, ale svět všecken ve zlém leží.
Mun sani mu na Allah ne, mun kuma sani dukkan duniya tana hannun mugun nan.
20 A vímeť, že Syn Boží přišel a dal nám smysl, abychom poznali toho pravého, a jsmeť v tom pravém, i v Synu jeho Ježíši Kristu. Onť jest ten pravý Bůh a život věčný. (aiōnios )
Amma mun sani Dan Allah yazo, kuma ya bamu fahimta, domin mu san wanda yake shi ne mai gaskiya. Haka kuma muna cikin wannan wanda shine gaiskiya, kuma cikin Dansa Yesu Almasihu. Shine Allah na gaskiya, da kuma rai na har abada. (aiōnios )
21 Synáčkové, vystříhejte se modl. Amen.
'Ya'ya, ku tsare kanku daga bautar gumaka.