< Ruta 4 >
1 Boaz potom iziđe na gradska vrata i sjede ondje. I gle, naiđe onaj skrbnik o kome je govorio. I dozva ga Boaz: “Ej, hodi ovamo i sjedni!” Onaj dođe i sjede.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Onda Boaz uze deset ljudi između starješina gradskih i reče: “Posjedajte ovdje!” I posjedaše.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 Zatim reče skrbniku: “Noemi, koja se vratila s Moapskih polja, htjela bi prodati ono zemlje našega brata Elimeleka.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 Zato sam odlučio da se s tobom razgovorim i predložim ti: otkupi njivu pred ovima koji sjede ovdje i pred starješinama moga naroda. Ako je kaniš otkupiti, onda otkupi; ako ne kaniš, kaži mi da znam. Jer prije tebe nema nitko pravo na otkup; ja sam na redu tek iza tebe.” A onaj reče: “Hoću, otkupit ću je.”
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Onda kaza Boaz: “Kad uzmeš zemlju iz ruke Noemi, treba da uzmeš i Rutu Moapku, pokojnikovu ženu, da se pokojniku sačuva ime na baštini.”
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 Ali skrbnik reče: “E, onda ne mogu biti otkupnik, da ne raspem svoje baštine. Otkupi ti po svome skrbničkom pravu jer ja ne mogu.”
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 A bijaše od starine običaj u Izraelu: da se čemu potkrijepi valjanost otkupa ili zamjene, čovjek bi izuo sandalu i dao je drugome. To bijaše svjedočanstvo u Izraelu.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Tako dakle i onaj skrbnik reče Boazu: “Otkupi ti!” te izu sandalu i dade mu je.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 Tada Boaz kaza starješinama i svemu narodu: “Vi ste danas svjedoci da ja otkupljujem iz ruke Noemine sve ono što je bilo Elimelekovo, sve što je bilo Kiljonovo i Mahlonovo.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 Uz to uzimam za ženu Rutu Moapku, ženu Mahlonovu, da bi se sačuvalo ime pokojnikovo na baštini i da se ime njegovo ne bi zatrlo među braćom njegovom i nestalo s vrata zavičaja njegova. Vi ste danas tome svjedoci.”
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 Sav narod koji se nalazio na vratima gradskim i starješine rekoše: “Svjedoci smo! Dao Jahve da žena koja ulazi u dom tvoj bude kao Rahela i Lea, koje su obje podigle kuću Izraelovu! Obogati se u Efrati, a prodiči u Betlehemu!
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 Neka tvoja kuća, po potomstvu koje će ti dati Jahve od ove mlade žene, bude kao kuća Peresa, koga Judi rodi Tamara!”
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 Tako Boaz uze Rutu i ona posta žena njegova. Uđe on k njoj i Jahve joj dade te ona zatrudnje i rodi sina.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 Onda žene rekoše Noemi: “Blagoslovljen bio Jahve koji ti danas nije uskratio skrbnika! I prodičio njegovo ime u Izraelu!
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 On će biti tvoja utjeha i potpora starosti tvojoj; jer ga rodi snaha tvoja koja te ljubi i koja ti vrijedi više od sedam sinova.”
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 Noemi uze dječaka, metnu ga sebi na krilo i bi mu odgojiteljicom.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 Susjede mu nadjenuše ime govoreći: “Noemi se rodio sin!” I prozvaše ga Obed; on je otac Jišaja, oca Davidova.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 A ovo je rodoslovlje Peresovo: Peres imade sina Hesrona,
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 Hesron Rama, Ram Aminadaba,
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 Aminadab Nahšona, Nahšon Salmona,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 Salmon Boaza, Boaz Obeda,
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 Obed Jišaja, a Jišaj Davida.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.