< Otkrivenje 2 >

1 Anđelu Crkve u Efezu napiši: “Ovo govori Onaj koji drži sedam zvijezda u desnici, Onaj koji stupa posred sedam zlatnih svijećnjaka:
''Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Afisus, ka rubuta: 'Wadannan sune kalmomin wanda ke rike da taurari bakwai a cikin hannun damarsa. wanda yake tafiya a tsakanin zankayen fitilun zinari bakwai,
2 Znam tvoja djela, tvoj trud i postojanost tvoju i da ne možeš podnijeti opakih. Iskušao si one koji se prave apostolima, a nisu, i otkrio si da su lažljivci.
''Na san abubuwan da ka yi, da famar ka, da hakurinka da jimirinka. Na sani ba ka jimrewa miyagun mutane, na sani ka gwada wadanda suka ce da kansu, su manzanni ne, amma ba haka ba, ka tarar da su makaryata.
3 Postojan si, podnio si za ime moje i nisi smalaksao.
Na san kana da tsawon jimrewa, kuma ka sha wahala sosai sabili da sunana, kuma baka gaji ba.
4 Ali imam protiv tebe: prvu si ljubav svoju ostavio.
Amma ga rashin jin dadi na da kai, ka bar kaunar ka ta fari.
5 Spomeni se dakle odakle si pao, obrati se i čini prva djela. Inače dolazim k tebi i - uklonit ću tvoj svijećnjak s mjesta njegova ako se ne obratiš.
Domin haka ka tuna daga inda ka fadi. Ka tuba ka yi abubuwan da ka yi da fari. Sai fa ka tuba, zan zo maka in kuma cire fitilar ka daga mazauninta.
6 Ali ovo imaš: mrziš nikolaitska djela koja i ja mrzim.”
Amma kana da wannan: Ka tsani abubuwan da Nikolatawa suka yi, wanda nima na tsana.
7 “Tko ima uho, nek posluša što Duh govori crkvama! Pobjedniku ću dati jesti od stabla života koje je u raju Božjem.”
wanda yake da kunnen ji ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bashi dama ya ci daga itacen rai, wanda ke cikin firdausin Allah.””
8 I anđelu Crkve u Smirni napiši: “Ovo govori Prvi i Posljednji, Onaj koji bijaše mrtav i oživje:
Zuwa ga mala'ikan da ke Ikilisiliyar Samirna rubuta: 'Wadannan su ne kalmomin wanda yake shine farko shine karshe, wanda ya mutu ya sake rayuwa kuma.
9 Znam tvoju nevolju i siromaštvo - ali ti si bogat! - i pogrde od onih koji se nazivaju Židovima, a nisu, nego su sinagoga Sotonina.
''Na san wahalun ka da talaucin ka amma kana da arziki. Nasan masu bata suna wadanda suke cewa su Yahudawa ne, amma ba haka suke ba. Su majami'ar Shaidan ne.
10 Ne boj se onoga što ti je trpjeti! Evo, Sotona, će neke od vas baciti u tamnicu da budete iskušani. Bit ćete u nevolji deset dana. Budi vjeran do smrti i dat ću ti vijenac života.”
Kada ka ji tsoron wahalar da zaka fuskanta nan gaba. Duba! Shaidan yana gab da jefa wadansun ku cikin kurkuku, domin a gwada ku, kuma zaku sha wahala ta kwana goma. Kuyi aminci har ga mutuwa zan baku rawanin rai.
11 “Tko ima uho, nek posluša što Duh govori crkvama! Pobjedniku neće nauditi druga smrt.”
wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fada wa ikilisiyoyi. Shi wanda yayi nasara ba zai cutu a mutuwa ta biyu ba.””
12 I anđelu Crkve u Pergamu napiši: “Ovo govori Onaj u koga je mač dvosjek, oštar:
''Zuwa ga mala'ikan dake ikilisiyar Burgamas rubuta: 'Wadannan ne kalmomin wanda ya ke da takobi mai kaifi biyu;
13 Znam gdje prebivaš - ondje gdje je Sotonino prijestolje - a čvrsto se držiš moga imena te nisi zanijekao moje vjere ni u one dane kad je Antipa, moj svjedok, vjerni moj, ubijen kod vas - gdje Sotona prebiva.
''Na san inda kake zama can inda kursiyin shaidan yake. Duk da haka ka rike sunana da karfi, na sani baka yi musun bangaskiyar ka da ni ba, ko a lokacin Antifas mashaidina, amintaccena, wanda aka kashe a tsakaninku, can inda shaidan yake zama.
14 Ali imam nešto malo protiv tebe: imaš ondje nekih što drže nauk Bileama što pouči Balaka da stupicu stavi sinovima Izraelovim te blaguju od mesa žrtvovana idolima i bludu se podadu.
Amma ga rashin jin dadi na kadan da kai: Kana da wadansu da suke rike da koyarwar Bil'amu kamkam, wanda ya koya wa Balak ya sa abin tuntubi gaban 'ya'yan Isra'ila, domin su ci abincin da aka mika wa gumaka kuma suyi fasikanci.
15 Tako i ti imaš takvih koji drže nauk nikolaitski.
Hakannan kuma wasunku sun rike koyarwar Nikolatawa kamkam.
16 Obrati se dakle! Inače dolazim ubrzo k tebi da ratujem s njima mačem usta svojih.”
Sabili da haka ka tuba! Idan ka ki zan zo gare ka da sauri, kuma in yi yaki gaba da su da takobi dake cikin bakina.
17 “Tko ima uho, nek posluša što Duh govori crkvama! Pobjedniku ću dati mane sakrivene i bijel ću mu kamen dati, a na kamenu napisano ime novo koje nitko ne zna doli onaj koji ga prima.”
Bari wanda yake da kunne ya sauriri abin da Ruhu yake fadawa ikilisiyoyi. Ga wanda yayi nasara zan bada wata boyayyar manna, kuma zan bashi farin dutse da sabon suna a rubuce a kan dutsen, suna wanda ba wanda ya sani, sai shi wanda ya karbe shi.””
18 I anđelu Crkve u Tijatiri napiši: “Ovo govori Sin Božji, Onaj u koga su oči kao plamen ognjeni, a noge mu nalik na mjed uglađenu:
Zuwa ga mala'ikan ikilisiyar Tiyatira rubuta: 'Wadannan sune kalamomin Dan Allah, wanda yake da idanu kamar harshen wuta; sawayen kamar gogaggiyar tagulla:
19 Znam tvoja djela: tvoju ljubav, i vjeru, i služenje, i postojanost - i tvoja posljednja djela obilatija od prvašnjih.
''Na san abin da ka yi, kaunar ka, da bangaskiya da hidima da tsawon jimrewar ka. Na san abinda ka yi bada dadewa ba ya fi abinda ka yi da fari.
20 Ali imam protiv tebe: puštaš ženu Jezabelu, koja se pravi proročicom, da uči i zavodi moje sluge te se bludu podaju i blaguju od mesa žrtvovana idolima.
Amma ga rashin jin dadi na da kai: Kana hakurce wa matar nan Yezebel, wadda take kiran kanta annabiya. Ta wurin koyarwarta, ta rudi bayina suyi fasikanci kuma su ci abincin da aka mika wa gumaka sadaka.
21 Dadoh joj vremena za obraćenje, ali ona neće da se obrati od bludnosti svoje.
Na bata lokaci domin ta tuba amma bata so ta tuba da fasikancin ta.
22 Evo, bacam je na postelju, a bludne drugare njene u veliku nevolju ako se ne odvrate od njezinih djela;
Duba! zan jefa ta a kan gadon jinya, wadanda kuma suka yi zina da ita za su shiga babbar wahala, sai dai in sun tuba daga ayukan ta.
23 i djecu ću joj smrću pobiti. I znat će sve crkve: Ja sam Onaj koji istražuje bubrege i srca - i dat ću vam svakomu po djelima.
Zan buga 'ya'yanta da mutuwa, kuma dukan ikilisiyoyi zasu san cewa nine wanda nake bincike tunani da zukata. Zan ba kowanen ku bisa ga ayyukansa.
24 Vama pak velim - vama drugim u Tijatiri koji ne drže ovog nauka te ne upoznaše takozvanih dubina sotonskih: Ne stavljam na vas drugoga bremena
Amma ga sauran ku dake cikin Tayatira, ga kowanen ku wanda bai rike wannan koyarwar ba, kuma bai san abinda wadansu suke kira zurfafan abubuwan Shaidan ba—ga ku na ce ban sa muku wata nawaya ba.'
25 nego - što imate, čvrsto držite dok ne dođem.”
Duk da haka dole ku tsaya da karfi har in zo.
26 “Pobjedniku, onomu što do kraja bude vršio moja djela, dat ću vlast nad narodima
Wanda yayi nasara da wanda ya yi abin da na yi har karshe, a gareshi zan bada iko akan al'ummai
27 i vladat će njima palicom gvozdenom, kao posuđe glineno satirati ih -
Zai yi mulkin su da sandar karfe, zai farfasa su kamar randunan yumbu.”
28 kao što i ja to primih od Oca svoga. I dat ću mu zvijezdu Danicu.
Kamar yadda na karba daga wurin Ubana, ni kuma zan bashi tauraron asubahi.
29 Tko ima uho, nek posluša što Duh govori crkvama!”
Bari wanda yake da kunne ya saurari abinda Ruhu yake fadawa ikilisiyioyi.””

< Otkrivenje 2 >