< Psalmi 83 >
1 Pjesma. Psalam. Asafov. Ne šuti, Jahve, ne budi nijem i nemoj mirovati, Bože!
Waƙa ce. Zabura ta Asaf. Ya Allah, kada ka yi shiru; kada ka tsaya cik, ya Allah, kada ka daina motsi.
2 Jer evo: dušmani tvoji buče, i mrzitelji tvoji glave podižu.
Dubi yadda abokan gābanka suke fariya, dubi yadda maƙiyanka suke ɗaga kansu.
3 Protiv naroda se tvoga rote i svjetuju se protiv štićenika tvojih.
Da wayo suna ƙulle-ƙulle a kan mutanenka; suna shirya maƙarƙashiya a kan waɗanda kake so.
4 Govore: “Dođite, zatrimo ih da ne budu narod, nek' se ime Izrael više ne spominje!”
Suna cewa, “Ku zo, bari mu hallaka su ɗungum a matsayin al’umma, don kada a ƙara tuna da sunan Isra’ila.”
5 Zaista, jednodušno se svjetuju i protiv tebe savez sklopiše:
Da zuciya ɗaya suka yi ƙulle-ƙulle tare; suka haɗa kai gāba da kai,
6 šatori edomski i Jišmaelci, Moapci i Hagrijci,
tentunan Edom da na mutanen Ishmayel, na Mowab da kuma na Hagirawa,
7 Gebal i Amon i Amalek, Filisteja sa stanovnicima Tira.
Gebal, Ammon da Amalek, Filistiya, tare da mutanen Taya.
8 I Asirci se s njima udružiše, pružiše ruke potomcima Lotovim.
Har Assuriya ma ta haɗa kai da su don ta ba da ƙarfi ga zuriyar Lot. (Sela)
9 Učini njima k'o Midjancima, k'o Siseri i Jabinu na potoku Kišonu:
Ka yi musu abin da ka yi wa Midiyan, yadda ka yi wa Sisera da Yabin a kogin Kishon,
10 koji padoše blizu En-Dora i postaše gnojivo njivi.
waɗanda suka hallaka a En Dor suka zama kamar juji a ƙasa.
11 K'o Oreb i Zeb neka budu knezovi njihovi, kao Zebah i Salmuna nek' budu sve vođe njihove
Ka mai da manyansu kamar Oreb da Zeyib, dukan sarakunansu kamar Zeba da Zalmunna,
12 koji jednodušno vikahu: “Osvojimo krajeve Božje!”
waɗanda suka ce, “Bari mu mallaki wuraren kiwon Allah.”
13 Daj, o Bože, da budu kao kovitlac, kao pljeva koju nosi vjetar.
Ka mai da su kamar ɗan tsiron da kan karye, iska ta yi ta turawa, ya Allahna, kamar yayin da iska take hurawa,
14 Kao što oganj proždire šumu, kao što plamen sažiže bregove,
kamar yadda wuta ke cin kurmi ko harshen wutar da take ci a kan duwatsu,
15 tako ih goni olujom svojom, prestravi ih svojom žestinom!
haka za ka kore su da iska mai ƙarfi ka kuma firgita su da guguwarka.
16 Pokrij im lice sramotom, da traže tvoje ime, Jahve!
Ka rushe fuskokinsu da kunya don mutane su nemi sunanka, ya Ubangiji.
17 Neka se stide i plaše navijek, neka se posrame i neka izginu!
Bari su kasance cikin kunya da taƙaici; bari su hallaka cikin wulaƙanci.
18 Nek' znaju: ti si komu je ime Jahve, jedini Višnji nada svom zemljom.
Bari su san cewa kai, wanda sunansa ne Ubangiji, cewa kai kaɗai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya.