< Psalmi 71 >

1 Tebi si, Jahve, utječem, ne daj da se ikada postidim!
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 U pravdi me svojoj spasi i izbavi, prikloni uho k meni i spasi me!
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Budi mi hrid utočišta i čvrsta utvrda spasenja: jer ti si stijena i utvrda moja.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Bože moj, istrgni me iz ruke zlotvora, iz šake silnika i tlačitelja:
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 jer ti si, o Gospode, ufanje moje, Jahve, uzdanje od moje mladosti!
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 Na te se oslanjam od utrobe; ti si mi zaštitnik od majčina krila: u te se svagda uzdam.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 Mnogima postadoh čudo, jer ti si mi bio silna pomoć.
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 Usta mi bijahu puna tvoje hvale, slaviše te svaki dan!
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Ne zabaci me u starosti: kad mi malakšu sile, ne zapusti me!
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 Jer govore o meni moji dušmani, i koji me vrebaju složno se svjetuju:
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 “Bog ga je napustio; progonite ga i uhvatite jer nema tko da ga spasi!”
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 O Bože, ne stoj daleko od mene, Bože moj, pohitaj mi u pomoć!
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 Neka se postide i propadnu koji traže moj život; nek' se sramotom i stidom pokriju koji mi žele nesreću!
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 A ja ću se uvijek uzdati, iz dana u dan hvaleć' te sve više.
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 Ustima ću naviještati pravednost tvoju, povazdan pomoć tvoju: jer im ne znam broja.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 Kazivat ću silu Jahvinu, Gospode, slavit ću samo tvoju pravednost.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 Bože, ti mi bijaše učitelj od mladosti moje, i sve do sada naviještam čudesa tvoja.
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 Ni u starosti, kad posijedim, Bože, ne zapusti me, da kazujem mišicu tvoju naraštaju novom i svima budućima silu tvoju,
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 i pravednost tvoju, Bože, koja seže do neba, kojom učini velika djela. Bože, tko je kao ti!
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 Trpljenja mnoga i velika bacio si na me: ali ti ćeš me opet oživiti i opet me podići iz dubine zemlje.
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 Povećaj dostojanstvo moje i opet me utješi:
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 A ja ću uz harfu slaviti tvoju vjernost, o Bože, svirat ću ti u citaru, Sveče Izraelov!
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 Moje će usne klicati pjevajuć' tebi i moja duša koju si spasio.
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 I moj će jezik svagda slaviti pravdu tvoju, jer su postiđeni i posramljeni oni što traže moju nesreću.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Psalmi 71 >