< Psalmi 135 >
1 Aleluja! Hvalite ime Jahvino, hvalite, sluge Jahvine
Yabi Ubangiji. Yabi sunan Ubangiji; yabe shi, ku bayin Ubangiji,
2 koji u Domu Jahvinu stojite u predvorjima Doma Boga našega!
ku waɗanda kuke hidima a gidan Ubangiji, cikin filayen gidan Allahnmu.
3 Hvalite Jahvu jer dobar je Jahve, pjevajte imenu njegovu jer je ljupko!
Yabi Ubangiji, gama Ubangiji nagari ne; rera yabo ga sunansa, gama wannan yana da kyau.
4 Jer Jahve sebi odabra Jakova, Izraela za dragu svojinu.
Gama Ubangiji ya zaɓi Yaƙub ya zama nasa, Isra’ila ya zama mallakarsa mai daraja.
5 Znadem da je velik Jahve, da je nad bozima svim gospodar.
Na san cewa Ubangiji yana da girma, cewa shugabanmu ya fi dukan alloli girma.
6 Što god se Jahvi svidi, to čini na nebu i na zemlji, na moru i u bezdanima.
Ubangiji yana yin abin da ya ga dama, a sammai da kuma a duniya, cikin tekuna da kuma cikin dukan zurfafansu.
7 Oblake diže s kraja zemlje; stvara kiši munje, vjetar izvodi iz skrovišta njegovih.
Yakan sa gizagizai su taso daga iyakokin duniya; yakan aika da walƙiya tare da ruwan sama ya fito da iska daga ɗakunan ajiyarsa.
8 On Egiptu pobi prvorođence, ljude i stoku podjednako.
Ya kashe’ya’yan fari na Masar,’ya’yan fari na mutane da na dabbobi.
9 On učini znamenja i čudesa usred tebe, Egipte, protiv Faraona i svih slugu njegovih.
Ya aiko da alamu da abubuwan banmamaki a tsirkiyarku, ya Masar, a kan Fir’auna da kuma dukan bayinsa.
10 On pobi narode mnoge i pogubi kraljeve moćne:
Ya bugi al’ummai masu yawa ya kuma karkashe manyan sarakuna,
11 Sihona, kralja amorejskog, i Oga, kralja bašanskog, i sva kraljevstva kanaanska.
Sihon sarkin Amoriyawa, Og sarkin Bashan da kuma dukan sarakunan Kan’ana,
12 I dade njihovu zemlju u baštinu, u baštinu Izraelu, narodu svom.
ya kuma ba da ƙasarsa kamar abin gādo, abin gādo ga mutanensa Isra’ila.
13 Ime tvoje, o Jahve, ostaje dovijeka i spomen na te, o Jahve, od koljena do koljena.
Sunanka, ya Ubangiji, dawwammame ne har abada, sanin da aka yi maka, ya Ubangiji, yana nan cikin dukan zamanai.
14 Jer Jahve štiti narod svoj, slugama svojim on je milostiv.
Gama Ubangiji zai nuna cewa mutanensa ba su da laifi ya kuma ji tausayin bayinsa.
15 Kumiri poganski, srebro i zlato, ljudskih su ruku djelo:
Gumakan al’ummai azurfa ne da zinariya, da hannuwan mutane suka yi.
16 usta imaju, a ne govore; oči imaju, a ne vide;
Suna da bakuna, amma ba sa magana, idanu, amma ba sa gani;
17 uši imaju, a ne čuju; i nema daha u ustima njihovim.
suna da kunnuwa, amma ba sa ji, ba kuwa numfashi a bakunansu.
18 Takvi su i oni koji ih napraviše i svi koji se u njih uzdaju.
Waɗanda suka yi su za su zama kamar su, haka kuma zai zama da dukan waɗanda suke dogara gare su.
19 Dome Izraelov, Jahvu blagoslivljaj! Dome Aronov, Jahvu blagoslivljaj!
Ya gidan Isra’ila, yabi Ubangiji; Ya gidan Haruna, yabi Ubangiji;
20 Dome Levijev, Jahvu blagoslivljaj! Štovatelji Jahvini, Jahvu blagoslivljajte!
Ya gidan Lawi, yabi Ubangiji; ku da kuke tsoronsa, yabi Ubangiji.
21 Blagoslovljen sa Siona Jahve koji prebiva u Jeruzalemu!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji daga Sihiyona, gare shi wanda yake zama a Urushalima. Yabi Ubangiji.