< Psalmi 102 >

1 Molitva nevoljnika koji je klonuo pa svoju tugu izlijeva Jahve, usliši molitvu moju, i vapaj moj k tebi da dođe!
Addu’ar mutum mai shan wahala. Sa’ad da ya rasa ƙarfi ya kuma yi makoki a gaban Ubangiji. Ka ji addu’ata, ya Ubangiji; bari kukata ta neman taimako ta zo gare ka.
2 Nemoj sakrivati lice od mene u dan moje nevolje! Prigni k meni uho svoje: kad te prizovem, brzo me usliši!
Kada ka ɓoye fuskarka daga gare ni sa’ad da nake cikin damuwa. Ka juye kunnenka gare ni; sa’ad da na yi kira, ka amsa mini da sauri.
3 Jer moji dani nestaju poput dima, a moje kosti gore kao oganj.
Gama kwanakina sun ɓace kamar hayaƙi; ƙasusuwana suna ƙuna kamar jan wuta.
4 Srce mi se suši kao pokošena trava i kruh svoj zaboravljam jesti.
Zuciyata ta kamu da ciwo ta kuma bushe kamar ciyawa; na manta in ci abinci.
5 Od snažnih jecaja mojih kosti mi uz kožu prionuše.
Saboda nishina mai ƙarfi na rame na bar ƙasusuwa kawai.
6 Sličan sam čaplji u pustinji, postah k'o ćuk na pustoj razvalini.
Ni kamar mujiyar jeji ne, kamar mujiya a kufai.
7 Ne nalazim sna i uzdišem k'o samotan vrabac na krovu.
Na kwanta a faɗake; na zama kamar tsuntsun da yake shi kaɗai a kan rufin ɗaki.
8 Svagda me grde dušmani moji; mnome se proklinju što bjesne na me.
Dukan yini abokan gābana suna tsokanata; waɗanda suke mini ba’a suna amfani da sunana yă zama abin la’ana.
9 Pepeo jedem poput kruha, a piće svoje miješam sa suzama
Gama ina cin toka a matsayin abincina ina kuma gauraye abin sha nawa da hawaye
10 zbog tvoje ljutine i gnjeva, jer si me digao i bacio.
saboda fushinka mai girma, gama ka ɗaga ni sama ka yar a gefe.
11 Moji su dani k'o oduljena sjena, a ja se, gle, sušim poput trave.
Kwanakina suna kamar inuwar yamma; na bushe kamar ciyawa.
12 A ti, o Jahve, ostaješ dovijeka i tvoje ime kroza sva koljena.
Amma kai, ya Ubangiji, kana zaune a kursiyinka har abada; sunan da ka yi zai dawwama a dukan zamanai.
13 Ustani, smiluj se Sionu: vrijeme je da mu se smiluješ - sada je čas!
Za ka tashi ka kuma ji tausayin Sihiyona, gama lokaci ne na nuna alheri gare ta; ƙayyadadden lokacin ya zo.
14 Jer milo je slugama tvojim kamenje njegovo, žale ruševine njegove.
Gama duwatsunta suna da daraja ga bayinka; ƙurarta kawai kan sa su ji tausayi.
15 Tad će se pogani bojati, Jahve, imena tvojega i svi kraljevi zemlje slave tvoje
Al’ummai za su ji tsoron sunan Ubangiji, dukan sarakunan duniya za su girmama ɗaukakarka.
16 kad Jahve opet sazda Sion, kad se pokaže u slavi svojoj,
Gama Ubangiji zai sāke gina Sihiyona ya kuma bayyana a ɗaukakarsa.
17 kad se osvrne na prošnju ubogih i ne prezre molitve njihove.
Zai amsa addu’ar marasa ƙarfi; ba zai ƙyale roƙonsu ba.
18 Nek' se zapiše ovo za budući naraštaj, puk što nastane neka hvali Jahvu.
Bari a rubuta wannan don tsara mai zuwa, cewa mutanen da ba a riga an halitta ba za su yabi Ubangiji,
19 Jer Jahve gleda sa svog uzvišenog svetišta, s nebesa na zemlju gleda
“Ubangiji ya duba ƙasa daga wurinsa mai tsarki a bisa, daga sama ya hangi duniya,
20 da čuje jauke sužnjeva, da izbavi smrti predane,
don yă ji nishe-nishen’yan kurkuku yă kuma saki waɗanda aka yanke musu hukuncin mutuwa.”
21 da se na Sionu navijesti ime Jahvino i njegova hvala u Jeruzalemu
Saboda haka za a furta sunan Ubangiji a Sihiyona yabonsa kuma a Urushalima
22 kad se narodi skupe i kraljevstva da služe Jahvi.
sa’ad da mutane da mulkoki suka tattaru don su yi wa Ubangiji sujada.
23 Putem je istrošio sile moje, skratio mi dane.
Cikin rayuwata, ya karye ƙarfina; ya gajartar da kwanakina.
24 Rekoh: “Bože moj, nemoj me uzeti u sredini dana mojih! Kroza sva koljena traju godine tvoje.
Sai na ce, “Kada ka ɗauke ni a tsakiyar kwanakina, ya Allah; shekarunka suna bi cikin dukan zamanai.
25 U početku utemelji zemlju, i nebo je djelo ruku tvojih.
A farkon fari ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
26 Propast će, ti ćeš ostati, sve će ostarjeti kao odjeća. Mijenjaš ih poput haljine i nestaju:
Za su hallaka, amma za ka ci gaba; duk za su tsufe kamar riga. Kamar riga za ka canja su za a kuwa zubar da su.
27 ti si uvijek isti - godinama tvojim nema kraja.
Amma kana nan yadda kake, kuma shekarunka ba za su taɓa ƙarewa ba.
28 Djeca će tvojih slugu živjeti u miru i potomstvo će njihovo trajati pred tobom.
’Ya’yan bayinka za su zauna a gabanka; zuriyarsu za su kahu a gabanka.”

< Psalmi 102 >