< Mudre Izreke 28 >
1 Opaki bježe i kad ih nitko ne progoni, a pravednici su neustrašivi kao mladi lav.
Mugu yakan gudu ko babu wanda yake korarsa, amma adalai suna da ƙarfin hali kamar zaki.
2 Kad se u zemlji griješi, mnogi su joj knezovi, a s čovjekom razumnim i umnim uprava je postojana.
Sa’ad da ƙasa ta yi tayarwa, takan kasance da masu mulki da yawa, amma mai fahimi da sani kan mai da zaman lafiya.
3 Čovjek opak koji tlači ubogoga - kiša je razorna poslije koje kruha nema.
Mai mulkin da ya danne talakawa yana kama da ruwan saman da ya lalatar da hatsi.
4 Koji zapuštaju Zakon, veličaju opake, a koji se drže Zakona, protive im se.
Duk waɗanda ba sa bin doka yabon mugaye suke yi, amma waɗanda suke yin biyayya da doka suna gāba da mugaye ke nan.
5 Zli ljudi ne razumiju pravice, a koji traže Jahvu, razumiju sve.
Mugaye ba su san gaskiya ba, amma waɗanda suke neman Ubangiji sun santa sosai.
6 Bolji je siromah koji živi bezazleno nego bogataš koji kroči krivim putem.
Gara matalauci wanda yake tafiya babu abin zargi da mai arziki wanda hanyoyinsa mugaye ne.
7 Tko se drži Zakona, razuman je sin, a tko se druži s izbjeglicama, sramoti oca svoga.
Duk wanda ya kiyaye doka ɗa ne mai la’akari, amma wanda yake abokantaka da masu zari yakan jawo wa mahaifinsa kunya.
8 Tko umnožava bogatstvo svoje lihvom i pridom, skuplja ga onomu tko je milostiv ubogima.
Duk wanda ya tara dukiyarsa ta wurin ba da bashi da ruwan da ya wuce misali yana tara wa wani ne wanda zai yi wa talakawa alheri.
9 Tko uklanja uho svoje da ne sluša Zakona, i molitva je njegova mrska.
In wani ya yi kunnuwa ƙashi ga doka ko addu’arsa ma abar ƙyama ce.
10 Tko zavodi poštene na put zao, past će u jamu svoju, a pošteni će baštiniti sreću.
Duk wanda ya jagorance masu aikata gaskiya a hanyar mugunta zai fāɗa cikin tarkonsa amma marasa abin zargi za su sami gādo mai kyau.
11 Bogat se čovjek čini sebi mudrim, ali će ga razuman siromah raskrinkati.
Mai arziki zai yi zato shi mai hikima ne a ganinsa, amma matalauci mai basira ya fi shi sanin abin da yake daidai.
12 Velika je slava kad se raduju pravednici, a kad se dižu opaki, ljudi se kriju.
Sa’ad da adalai suka yi nasara, kowa yakan yi biki; amma sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya.
13 Tko skriva svoje grijehe, nema sreće, a tko ih ispovijeda i odriče ih se, milost nalazi.
Duk wanda ya ɓoye zunubansa ba ya taɓa cin nasara, amma duk wanda ya furta ya kuma ƙi su yakan sami jinƙai.
14 Blago čovjeku uvijek bojaznu, jer čovjek okorjela srca zapada u nesreću.
Mai albarka ne mutumin da kullum yake jin tsoron Allah, amma duk wanda ya taurare zuciyarsa yakan shiga wahala.
15 Lav koji riče i gladan medvjed: takav je opak vladalac siromašnu narodu.
Kamar rurin zaki ko sanɗar beyar haka mugun mutum mai mulki a kan mutane marasa ƙarfi yake.
16 Nerazuman knez čini mnoga nasilja, a koji mrzi lakomost, dugo živi.
Mugu mai mulki ba shi da azanci, amma duk wanda yake ƙin ƙazamar riba yakan yi tsawon rai.
17 Onaj koga tišti krvna krivica, do groba bježi: ne zaustavljajte ga.
Mutumin da laifin kisa ya yi ta damunsa zai zama mai gudu don tsoro har mutuwa; kada wani ya taimake shi.
18 Spasava se tko živi pravedno, tko se koleba između dva puta, propada na jednom od njih.
Duk wanda ya yi tafiya marar abin zargi zai zauna lafiya, amma duk wanda hanyoyinsa mugaye ne zai fāɗi nan da nan.
19 Tko obrađuje svoju zemlju, nasitit će se kruha, a tko trči za tlapnjama, nasitit će se siromaštva.
Duk wanda ya nome gonarsa zai sami amfani a yalwace, amma duk wanda yake zaman banza zai zama matalauci a koyaushe.
20 Čestit čovjek stječe blagoslov, a tko hrli za bogatstvom, ne ostaje bez kazne.
Mutum mai aminci zai cika da albarka, amma duk mai son yin arziki dare ɗaya zai sha hukunci.
21 Ne valja biti pristran na sudu, jer i za zalogaj kruha čovjek čini zlo.
Nuna sonkai ba shi da kyau, duk da haka mutum zai aikata abin da ba daidai ba saboda’yar ƙaramar rashawa.
22 Pohlepnik hrli za bogatstvom, a ne zna da će ga stići oskudica.
Mai rowa yana alla-alla ya yi arziki bai san cewa talauci ne ke jiransa ba.
23 Tko kori čovjeka, nalazi poslije veću milost nego onaj koji laska jezikom.
Duk wanda ya tsawata wa wani mutum zai sami yabo a ƙarshe fiye da wanda yake mai daɗin baki.
24 Tko pljačka oca svoga i majku svoju i veli: “Nije grijeh”, drug je razbojniku.
Duk wanda ya yi wa mahaifin ko mahaifiyarsa sata ya kuma ce, “Ai, ba laifi ba ne” abokin mai hallakarwa ne shi.
25 Lakomac zameće svađu, a tko se uzda u Jahvu, uspjet će.
Mai haɗama yakan jawo tā-da-na-zaune-tsaye, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai yi nasara.
26 Bezuman je tko se uzda u svoje srce, a spasava se tko živi mudro.
Duk mai dogara ga kansa wawa ne, amma duk wanda yake tafiya da hikima zai zauna lafiya.
27 Tko daje siromahu, ne trpi oskudicu; a tko odvraća oči svoje, bit će proklet.
Duk wanda yake bayarwa ga matalauta ba zai rasa kome ba, amma duk wanda bai kula da su ba yana samu la’ana masu yawa.
28 Kad se dižu opaki, ljudi se kriju, a kad propadaju, tad se množe pravednici.
Sa’ad da mugu ya samu shugabanci, mutane sukan yi ta ɓuya; amma sa’ad da mugu ya hallaka, adali kan ci gaba cikin arziki da lafiya.