< Mudre Izreke 2 >
1 Sine moj, ako primiš moje riječi i pohraniš u sebi moje zapovijedi,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 i uhom svojim osluhneš mudrost i obratiš svoje srce razboru;
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 jest, ako prizoveš razum i zavapiš za razborom;
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 ako ga potražiš kao srebro i tragaš za njim kao za skrivenim blagom -
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 tada ćeš shvatiti strah Gospodnji i naći ćeš Božje znanje.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 Jer Jahve daje mudrost, iz njegovih usta dolazi znanje i razboritost.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 On pravednicima pruža svoju pomoć, štit je onih koji hode u bezazlenosti.
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 Jer on štiti staze pravde i čuva pute svojih pobožnika.
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Tada ćeš shvatiti pravdu, pravicu, pravednost i sve staze dobra,
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 jer će mudrost ući u tvoje srce i spoznaja će obradovati tvoju dušu.
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Oprez će paziti na te i razboritost će te čuvati:
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 da te izbavi od zla puta, od varava čovjeka,
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 od onih koji ostavljaju staze poštenja te idu mračnim putovima;
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 koji se vesele čineći zlo i likuju u opačinama zloće;
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 kojih su staze krive i koji su opaki na svojim putovima;
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 da te izbavi od preljubnice i od tuđinke koja laska riječima;
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 koja ostavlja prijatelja svoje mladosti i zaboravlja zavjet svoga Boga
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 jer joj kuća tone u smrt i njezini putovi vode mrtvima.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 Tko god zalazi k njoj ne vraća se nikad i ne nalazi više putove života.
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Zato idi putem čestitih i drži se staza pravedničkih!
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 Jer samo će pravedni nastavati zemlju i bezazleni će ostati na njoj.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 A opake će zbrisati sa zemlje i bogohulnike iščupati iz nje.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.