< Mudre Izreke 1 >

1 Mudre izreke Salomona, sina Davidova, kralja izraelskog:
Karin maganar Solomon ɗan Dawuda, sarkin Isra’ila.
2 da se spozna mudrost i pouka, da se shvate razumne riječi;
Ga karin magana da za su taimake ka don samun hikima da horo; don ganewa kalmomi masu zurfi;
3 da se primi umna pouka, pravda i pravica i nepristranost;
don neman rayuwa ta horo da kuma ta hankali, kana yin abin da yake daidai, mai adalci da kuma wanda ya dace;
4 da se dade pamet neiskusnima, mladiću znanje i umijeće;
don sa marar azanci yă yi hankali, yă sa matasa su sani, su kuma iya rarrabewa,
5 kad mudar čuje, da umnoži znanje, a razuman steče mudrije misli;
bari masu hikima su saurara, su kuma ƙara ga saninsu, bari masu tunani kuma su sami jagora,
6 da razumije izreke i prispodobe, riječi mudraca i njihove zagonetke.
don su fahimci karin magana da kuma misalai, kalmomi da kuma kacici-kacici masu hikima.
7 Strah je Gospodnji početak spoznaje, ali ludi preziru mudrost i pouku.
Tsoron Ubangiji shi ne masomin ilimi, amma wawaye sun rena hikima da horo.
8 Poslušaj, sine moj, pouku oca svoga i ne odbacuj naputka svoje majke!
Ɗana, ka saurari umarnin mahaifinka kada kuma ka ƙyale koyarwar mahaifiyarka.
9 Jer će ti biti ljupki vijenac na glavi i ogrlica oko tvoga vrata.
Za su zama kayan ado don su inganta ka da kuma sarƙar wuya don su yi wa wuyanka ado.
10 Sine moj, ako te grešnici mame, ne pristaj;
Ɗana, in masu zunubi sun jarabce ka, kada ka yarda.
11 ako bi rekli: “Hodi s nama, da vrebamo krv, čekamo u zasjedi nevina ni za što;
In suka ce, “Zo mu tafi; mu yi kwanton ɓauna, mu nemi wani mu kashe, mu fāɗa wa marasa laifi;
12 da ih progutamo žive kao carstvo smrti i cijele kao one koji silaze u grob; (Sheol h7585)
mu haɗiye su da rai gaba ɗaya kamar kabari, kamar waɗanda suke gangarawa zuwa rami; (Sheol h7585)
13 naplijenit ćemo svakojaka blaga, napuniti svoje kuće plijenom;
za mu sami dukiya masu daraja iri-iri, mu kuma cika gidajenmu da ganima;
14 bacat ćeš s nama svoj ždrijeb, svi ćemo zajedno imati jednu kesu.”
ka haɗa kai da mu, za mu kuwa raba abin da muka sato”
15 Sine moj, ne idi s njima na put, makni nogu od njihove staze.
ɗana, kada ka tafi tare da su, kada ka taka ƙafarka a hanyarsu;
16 Jer na zlo trče svojim nogama i hite prolijevati krv.
gama ƙafafunsu kan yi sauri ga yin zunubi, suna saurin yin kisankai.
17 Jer uzalud je razapinjati mrežu pred očima svima pticama.
Ba shi da amfani a kafa tarko a idanun dukan tsuntsaye!
18 A oni vrebaju vlastitu krv, postavljaju zasjedu svojemu životu.
Waɗannan irin mutane kansu suke kafa wa tarko; ba sa kama kome, sai rayukansu!
19 Takva je sudba svih lakomih na ružan dobitak: on ih života stane.
Dukan waɗanda suke neman ribar da ba a samu a hanya mai kyau; ƙarshen wannan yakan ɗauke rayukansu.
20 Mudrost glasno uzvikuje na ulici, na trgovima diže svoj glas;
Hikima tana kira da ƙarfi a kan titi, tana ɗaga muryarta a dandalin taron jama’a;
21 propovijeda po bučnim uglovima, na otvorenim gradskim vratima govori svoje riječi:
tana kira da ƙarfi a kan tituna masu surutu, tana yin jawabinta a hanyoyin shiga gari.
22 “Dokle ćete, vi glupi, ljubiti glupost i dokle će podsmjevačima biti milo podsmijevanje, i dokle će bezumnici mrziti znanje?
“Har yaushe ku da kuke marasa azanci za ku ci gaba a hanyoyinku marasa azanci? Har yaushe ku masu ba’a za ku yi ta murna cikin ba’arku wawaye kuma ku ƙi ilimi?
23 Poslušajte moju opomenu! Gle, svoj duh pred vas izlijevam, hoću vas poučiti svojim riječima.
Da a ce kun saurari tsawatata, da na faɗa muku dukan abin da yake zuciyata in kuma sanar da ku tunanina.
24 Koliko sam vas zvala, a vi ste odbijali; pružala sam ruku, ali je nitko ne opazi.
Amma da yake kun ƙi ni sa’ad da na yi kira ba kuma wanda ya saurara sa’ad da na miƙa hannuna,
25 Nego ste odbacili svaki moj savjet i niste poslušali moje opomene;
da yake kun ƙi dukan shawarata ba ku kuma yarda da tsawatata ba,
26 zato ću se i ja smijati vašoj propasti, rugat ću se kad vas obuzme tjeskoba:
Zan yi muku dariya sa’ad da masifa ta same ku, zan yi muku ba’a sa’ad da bala’i ya same ku,
27 kad navali na vas strah kao nevrijeme i zgrabi vas propast kao vihor, kad navali na vas nevolja i muka.
sa’ad da bala’i ya sha kanku kamar hadiri, sa’ad da masifa ta share ku kamar guguwa, sa’ad damuwa da wahala suka mamaye ku.
28 Tada će me zvati, ali se ja neću odazvati; tražit će me, ali me neće naći.
“Sa’an nan za su kira gare ni amma ba zan amsa ba; za su neme ni amma ba za su same ni ba.
29 Jer su mrzili spoznaju i nisu izabrali Gospodnjeg straha
Da yake sun ƙi sani ba su kuwa zaɓi tsoron Ubangiji ba,
30 niti su poslušali moj savjet, nego su prezreli svaku moju opomenu.
da yake ba su karɓi shawarata ba suka kuwa yi kunnen ƙashi ga tsawatata,
31 Zato će jesti plod svojeg vladanja i nasititi se vlastitih savjeta.
za su sami sakayyar abubuwan da suka yi su kuma ƙoshi da sakayyar makircinsu.
32 Jer glupe će ubiti njihovo odbijanje, a nemar će upropastiti bezumne.
Gama rashin hankalin marasa azanci zai kashe su, rashin kulawar wawaye kuma zai hallaka su;
33 A tko sluša mene, bezbrižan ostaje i spokojno živi bez straha od zla.”
amma duk wanda ya saurare ni, zai zauna lafiya yă kuma kasance da rai kwance, ba tare da tsoron lahani ba.”

< Mudre Izreke 1 >