< Mihej 7 >
1 Teško meni! Postao sam kao žetelac ljeti, kao trgač poslije jematve: nema bobice grožđa da je pozobljem, nema smokve ranke za kojom žudim!
Tawa ta ƙare! Ina kama da wanda yake tattara’ya’yan itatuwa a lokacin kalar’ya’yan inabi; babu sauran nonon inabin da za a tsinka a ci, babu kuma’ya’yan ɓaure na farko-farkon da raina yake marmari.
2 Vjernici su iščezli iz zemlje: nijednog pravednika među ljudima! Svi vrebaju za krvoprolićem, svaki svome bratu mrežu postavlja.
An kawar da masu tsoron Allah daga ƙasar; babu sauran mai adalcin da ya rage. Dukan mutane suna kwanto don su zub da jini; kowa yana farautar ɗan’uwansa da tarko.
3 Njihove ruke za zlo su sposobne: glavar traži dar, sudac sudi prema poklonu, velikaš po svome hiru odlučuje.
Dukan hannuwansu sun gwaninta wajen yin mugunta; shugabanni suna nema a ba su kyautai, alƙalai suna nema a ba su cin hanci, masu iko suna faɗar son zuciyarsu, duk suna ƙulla makirci tare.
4 I najbolji među njima je kao trn, najpravedniji kao drača živica. Iskušenje njihovo danas sa Sjevera dolazi, dolazi ura strave njihove.
Mafi kyau a cikinsu yana kama da ƙaya, mafi gaskiyarsu ya fi shingen ƙaya muni. Ranar da Allah zai ziyarce ku ta zo, ranar da masu gadinku za su hura ƙaho. Yanzu ne lokacin ruɗewarku.
5 Ne pouzdavajte se u bližnjega, ne vjerujte u prijatelja; pred onom koja s tobom dijeli postelju pazi da usta ne otvoriš.
Kada ka yarda da maƙwabci; kada ka sa begenka ga abokai. Ko ma wadda take kwance a ƙirjinka, ka yi hankali da kalmominka.
6 Jer sin svoga oca zlostavlja, kćerka na majku ustaje, snaha na svoju svekrvu, svakome je dušmanin njegov ukućanin.
Gama ɗa yakan ce wannan ba mahaifinsa ba ne, diya kuma takan tayar wa mahaifiyarta, matar ɗa takan yi gāba da uwar mijinta, abokan gāban mutum su ne iyalin cikin gidansa.
7 A ja, prema Jahvi ja sam zagledan, čekam na Boga koji spasava, Bog moj mene će uslišati.
Amma game da ni, zan sa bege ga Ubangiji, ina sauraron Allah Mai Cetona; Allahna kuwa zai ji ni.
8 Ne raduj se mome zlu, dušmanko moja, ako sam pao, ustat ću; ako boravim u tminama, Jahve je svjetlost moja.
Kada ku yi farin ciki, ku maƙiyana! Ko da yake na fāɗi, zan tashi. Ko da yake na zauna a cikin duhu, Ubangiji zai zama haskena.
9 Moram podnositi srdžbu Jahvinu, jer sam protiv njega sagriješio, sve dok on ne prosudi spor moj i izrekne pravdu; izvest će me na svjetlost, gledat ću pravednost njegovu.
Domin na yi masa zunubi, zan fuskanci fushin Ubangiji, har sai ya dubi batuna ya kuma tabbatar da’yancina. Zai kawo ni zuwa wurin haske; zan ga adalcinsa.
10 Kada ga moja dušmanka ugleda, od stida će se pokriti ona koja mi je govorila: “Gdje je on, Jahve, tvoj Bog?” Moje će se oči naslađivati kad je ugledam: ona će biti zgažena kao blato na putu.
Sa’an nan maƙiyina zai gani yă kuma sha kunya, shi da yake ce da ni “Ina Ubangiji Allahnka?” Zai gani, yă kuma ji kunya. Ko yanzu ma za a tattake shi kamar taɓo a tituna.
11 Dolazi dan kad će se sazidati tvoji bedemi! Toga dana nadaleko će se prostirati tvoje granice!
Ranar gina katangarka tana zuwa, a ranar za a fadada iyakokinka.
12 Toga dana dolazit će k tebi od zemlje asirske do Egipta, od Tira do Rijeke, od mora do mora, od gore do gore.
A wannan rana mutane za su zo gare ka daga Assuriya da kuma biranen Masar, daga Masar ma har zuwa Yuferites daga teku zuwa teku, kuma daga dutse zuwa dutse.
13 Zemlja će postat' pustinja zbog stanovnika svojih, zbog djela njihovih.
Duniya za tă zama kufai saboda mazaunanta, saboda ayyukansu.
14 Pasi svoj narod svojom palicom, stado svoje baštine, koje osamljeno živi u šikarju, usred plodnih voćnjaka. Neka pase u Bašanu i Gileadu, kao u davne dane!
Ka yi kiwon mutanenka da sandarka, garken gādonka, wanda yake zaune shi kaɗai a kurmi, a ƙasa mai kyau ta kiwo, bari su yi kiwo a Bashan da Gileyad kamar a kwanakin dā.
15 Kao u dane kad si izašao iz Egipta, pokaži nam čudesa!
“Kamar a kwanakin da kuka fito daga Masar, zan nuna musu al’ajabaina.”
16 Narodi će ih vidjeti i bit će posramljeni uza svu silu svoju; stavit će ruku na usta i uši će im oglušiti.
Al’ummai za su gani su kuma ji kunya, za a kuma ƙwace musu dukan ikonsu. Za su kama bakinsu kunnuwansu kuma za su zama kurame.
17 Lizat će prašinu kao zmija, kao gmazovi koji gmižu po zemlji. Izići će dršćući iz svojih jazbina, prestravljeni i ustrašeni pred tobom.
Za su lashi ƙura kamar maciji, kamar dabbobi masu rarrafe a ƙasa. Za su fito daga maɓuyarsu da rawan jiki, za su juya cikin tsoro ga Ubangiji Allahnmu su kuma ji tsoronku.
18 Tko je Bog kao ti koji prašta krivnju, koji grijeh oprašta i prelazi preko prekršaja Ostatka baštine svoje, koji ne ustraje dovijeka u svome gnjevu, nego uživa u pomilovanju?
Wane ne Allah kamar ka, wanda yake yafe zunubi yă kuma gafarta laifofin mutanensa da suka ragu? Ba ka zama mai fushi har abada amma kana marmari ka nuna jinƙai.
19 Još jednom, imaj milosti za nas! Satri naše opačine, baci na dno mora sve grijehe naše!
Za ka sāke jin tausayinmu; za ka tattake zunubanmu a ƙarƙashin sawunka ka kuma tura dukan kurakuranmu zuwa cikin zurfafan teku.
20 Udijeli Jakovu vjernost svoju, dobrotu svoju Abrahamu, kako si se zakleo ocima našim od dana iskonskih.
Za ka yi wa Yaƙub aminci, ka kuma nuna jinƙai ga Ibrahim, kamar yadda ka yi alkawari da rantsuwa ga kakanninmu tun a kwanankin dā.