< Matej 6 >
1 “Pazite da svoje pravednosti ne činite pred ljudima da vas oni vide. Inače, nema vam plaće u vašeg Oca koji je na nebesima.
Ku yi hankali kada ku yi ayyukan adalcinku gaban mutane domin su ganku, idan kun yi haka, ba za ku sami sakamako a wurin Ubanku da yake sama ba.
2 Kada dakle dijeliš milostinju, ne trubi pred sobom, kako to u sinagogama i na ulicama čine licemjeri da bi ih ljudi hvalili. Zaista, kažem vam, primili su svoju plaću.
Saboda haka, in za ku yi sadaka, kada ku busa kaho yadda munafukai suke yi a majami'u da kuma akan tituna domin mutane su yabesu. Gaskiya ina gaya maku, sun samu ladansu.
3 Ti naprotiv, kada daješ milostinju - neka ti ne zna ljevica što čini desnica,
Amma in za ku yi sadaka, kada hannunku na hagu ya san abin da hannunku na dama yake yi,
4 da tvoja milostinja bude u skrovitosti. I Otac tvoj, koji vidi u skrovitosti, uzvratit će ti!”
domin sadakarku ta zama a asirce. Ubanku kuwa da yake ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku.
5 “Tako i kad molite, ne budite kao licemjeri. Vole moliti stojeći u sinagogama i na raskršćima ulica da se pokažu ljudima. Zaista, kažem vam, primili su svoju plaću.
Sa'adda za ku yi addu'a kuma, kada ku zama kamar munafukai, domin sun cika son yin addu'a a tsaye a majami'unsu da kuma a gefen tituna, domin mutane su gansu. Gaskiya ina gaya maku, sun sami ladarsu kenan.
6 Ti naprotiv, kad moliš, uđi u svoju sobu, zatvori vrata i pomoli se svomu Ocu, koji je u skrovitosti. I Otac tvoj, koji vidi u skrovitosti, uzvratit će ti.”
Amma ku, idan za ku yi addu'a, sai ku shiga cikin daki. Ku rufe kofa, ku yi addu'a ga Ubanku wanda yake a asirce, Ubanku kuwa da ke ganin abin da ake yi a asirce, zai saka maku.
7 “Kad molite, ne blebećite kao pogani. Misle da će s mnoštva riječi biti uslišani.
Idan za ku yi addu'a, kada ku yi ta maimaici marar anfani, kamar yadda al'ummai suke yi, domin a tunanin su za a saurare su saboda yawan maganganunsu.
8 Ne nalikujte na njih. Ta zna vaš Otac što vam treba i prije negoli ga zaištete.
Domin haka, kada ku zama kamarsu, domin Ubanku ya san bukatar ku tun kafin ku roke shi.
9 Vi, dakle, ovako molite: 'Oče naš, koji jesi na nebesima! Sveti se ime tvoje!
Saboda haka sai ku yi addu'a kamar haka: 'Ubanmu da ke sama, bari a tsarkake sunanka.
10 Dođi kraljevstvo tvoje! Budi volja tvoja kako na nebu tako i na zemlji!
Bari mulkinka shi zo. Bari nufinka ya yiwu a duniya kamar yadda ake yi a sama.
11 Kruh naš svagdanji daj nam danas!
Ka ba mu yau abincinmu na kullum.
12 I opusti nam duge naše kako i mi otpustismo dužnicima svojim!
Ka gafarta mana basussukanmu, kamar yadda mu ma muke gafarta ma wadanda muke bi bashi.
13 I ne uvedi nas u napast, nego izbavi nas od Zloga!'”
Kuma kada ka kawo mu cikin jaraba, amma ka kubutar da mu daga Mugun.' [Gama mulki da iko da daukaka naka ne har abada. Amin]
14 “Doista, ako vi otpustite ljudima njihove prijestupke, otpustit će i vama Otac vaš nebeski.
Domin in kun yafe wa mutane laifuffukansu, Ubanku na Sama shima zai yafe maku.
15 Ako li vi ne otpustite ljudima, ni Otac vaš neće otpustiti vaših prijestupaka.”
In kuwa ba ku yafe wa mutane laifuffukansu ba, Ubanku ma ba zai yafe muku laifuffukanku ba.”
16 “I kad postite, ne budite smrknuti kao licemjeri. Izobličuju lica da pokažu ljudima kako poste. Zaista, kažem vam, primili su svoju plaću.
Haka kuma, in za ku yi azumi, kada ku zama da fuska kamar masu makoki yadda munafukai ke yi, domin sukan yankwane fuskokinsu, domin su bayyana ga mutane kamar suna azumi. Gaskiya, ina gaya maku, sun sami ladansu ke nan.
17 Ti naprotiv, kad postiš, pomaži glavu i umij lice
Amma in kuna azumi, ku shafa mai a ka, ku kuma wanke fuska,
18 da ne zapaze ljudi kako postiš, nego Otac tvoj, koji je u skrovitosti. I Otac tvoj, koji vidi u skrovitosti, uzvratit će ti.”
don kada mutane su gane kuna azumi, sai dai Ubanku da yake a asirce. Kuma Ubanku da ke ganin abinda ke a asirce, zai saka maku.”
19 “Ne zgrćite sebi blago na zemlji, gdje ga moljac i rđa nagrizaju i gdje ga kradljivci potkapaju i kradu.
“Kada ku tara wa kanku dukiya a duniya, inda asu da tsatsa ke batawa, inda barayi kuma ke fasawa su yi sata.
20 Zgrćite sebi blago na nebu, gdje ga ni moljac ni rđa ne nagrizaju i gdje kradljivci ne potkapaju niti kradu.
Maimakon haka, ku tara wa kanku dukiya a sama, inda babu asu da tsatsa da za su bata, inda kuma ba barayi da za su fasa su yi sata.
21 Doista, gdje ti je blago, ondje će ti biti i srce.”
Domin inda dukiyar ka take, a nan zuciyar ka ma take.
22 “Oko je tijelu svjetiljka. Ako ti je dakle oko bistro, sve će tijelo tvoje biti svijetlo.
Ido shi ne fitilar jiki. Saboda haka, idan idonka na da kyau, dukan jiki na cike da haske.
23 Ako ti je pak oko nevaljalo, sve će tijelo tvoje biti tamno. Ako je dakle svjetlost koja je u tebi - tamna, kolika će istom tama biti?”
Amma in idonka na da lahani, dukan jiki na cike da duhu. Saboda haka, in hasken da yake cikinka duhu ne, ina misalin yawan duhun!
24 “Nitko ne može služiti dvojici gospodara. Ili će jednoga mrziti, a drugoga ljubiti; ili će uz jednoga prianjati, a drugoga prezirati. Ne možete služiti Bogu i bogatstvu.”
Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu, ko dai ya ki daya, ya so daya, ko kuma ya amince wa dayan ya raina dayan. Ba dama ku bauta wa Allah da kuma dukiya.
25 “Zato vam kažem: Ne budite zabrinuti za život svoj: što ćete jesti, što ćete piti; ni za tijelo svoje: u što ćete se obući. Zar život nije vredniji od jela i tijelo od odijela?”
Saboda haka ina gaya maku, kada ku damu a kan rayuwarku, game da abin da za ku ci, da abin da za ku sha- ko kuwa jikinku, abin da za ku yi tufafi da shi. Ashe rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba?
26 “Pogledajte ptice nebeske! Ne siju, ne žanju niti sabiru u žitnice, pa ipak ih hrani vaš nebeski Otac. Zar niste vi vredniji od njih?
Ku dubi tsuntsayen da ke sararin sama. Ai, ba su shuka, balle girbi, ba su kuma tarawa a cikin rumbuna, amma Ubanku na Sama na ciyar da su. Ashe, ba ku fi su martaba ba?
27 A tko od vas zabrinutošću može svome stasu dodati jedan lakat?
Kuma wanene a cikinku, don damuwarsa, zai iya kara ko taki ga tsawon rayuwarsa?
28 I za odijelo što ste zabrinuti? Promotrite poljske ljiljane, kako rastu! Ne muče se niti predu.
To, don me kuke damuwa a kan tufafi? Ku dubi furannin jeji, yadda suke girma. Ba su aiki, kuma ba su sakar kaya.
29 A kažem vam: ni Salomon se u svoj svojoj slavi ne zaodjenu kao jedan od njih.
Duk da haka ina gaya maku, ko Sulaimanu ma, cikin dukan daukakar sa bai yi ado kamar daya daga cikin wadannan ba.
30 Pa ako travu poljsku, koja danas jest a sutra se u peć baca, Bog tako odijeva, neće li još više vas, malovjerni?”
Idan Allah yayi wa ciyawar jeji ado, wadda yau tana wanzuwa, gobe kuwa a jefa ta cikin murhu, ina misalin adon da za ya yi maku, ya ku masu karancin bangaskiya?
31 “Nemojte dakle zabrinuto govoriti: 'Što ćemo jesti?' ili: 'Što ćemo piti?' ili: 'U što ćemo se obući?'
Don haka kada ku damu, kuna cewa, 'Me za mu ci? ko, Me za mu sha?' ko kuwa, 'Wadanne tufafi za mu sa?'
32 Ta sve to pogani ištu. Zna Otac vaš nebeski da vam je sve to potrebno.
Ai, al'ummai ma suna neman dukan irin wadannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu.
33 Tražite stoga najprije Kraljevstvo i pravednost njegovu, a sve će vam se ostalo dodati.
Amma ku nemi mulkinsa da farko da adalcinsa, kuma dukan wadannan abubuwa za a baku.
34 Ne budite dakle zabrinuti za sutra. Sutra će se samo brinuti za se. Dosta je svakom danu zla njegova.”
“Saboda haka kada ku damu don gobe, ai, gobe za ta damu da kanta. Kowace rana ta na cike da wahalarta”.