< Luka 1 >
1 Kad već mnogi poduzeše sastaviti izvješće o događajima koji se ispuniše među nama -
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 kako nam to predadoše oni koji od početka bijahu očevici i sluge Riječi -
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 pošto sam sve, od početka, pomno ispitao, naumih i ja tebi, vrli Teofile, sve po redu napisati
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 da se tako osvjedočiš o pouzdanosti svega u čemu si poučen.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 U dane Heroda, kralja judejskoga, bijaše neki svećenik imenom Zaharija iz razreda Abijina. Žena mu bijaše od kćeri Aronovih, a ime joj Elizabeta.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 Oboje bijahu pravedni pred Bogom: živjeli su besprijekorno po svim zapovijedima i odredbama Gospodnjim.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 No nisu imali djeteta jer Elizabeta bijaše nerotkinja, a oboje već poodmakle dobi.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 Dok je Zaharija jednom po redu svoga razreda obavljao svećeničku službu pred Bogom,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 ždrijebom ga zapade po bogoslužnom običaju da uđe u Svetište Gospodnje i prinese kad.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 Za vrijeme kađenice sve je ono mnoštvo naroda vani molilo.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 A njemu se ukaza anđeo Gospodnji. Stajao je s desne strane kadionoga žrtvenika.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 Ugledavši ga, Zaharija se prepade i strah ga spopade.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 No anđeo mu reče: “Ne boj se, Zaharija! Uslišana ti je molitva: žena će ti Elizabeta roditi sina. Nadjenut ćeš mu ime Ivan.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 Bit će ti radost i veselje i rođenje će njegovo mnoge obradovati.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 Bit će doista velik pred Gospodinom. Ni vina ni drugoga opojnog pića neće piti. Duha Svetoga bit će pun već od majčine utrobe.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 Mnoge će sinove Izraelove obratiti Gospodinu, Bogu njihovu.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 Ići će pred njim u duhu i sili Ilijinoj da obrati srce otaca k sinovima i nepokorne k razumnosti pravednih te spremi Gospodinu narod pripravan.”
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 Nato Zaharija reče anđelu: “Po čemu ću ja to razaznati. Ta star sam i žena mi poodmakle dobi.”
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 Anđeo mu odgovori: “Ja sam Gabriel koji stojim pred Bogom. Poslan sam da govorim s tobom i da ti donesem ovu radosnu poruku.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 I evo, budući da nisi povjerovao mojim riječima, koje će se ispuniti u svoje vrijeme, zanijemjet ćeš i nećeš moći govoriti do dana dok se to ne zbude.”
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 Narod je iščekivao Zahariju i čudio se što se toliko zadržao u Svetištu.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 Kad je napokon izašao, nije im mogao ništa reći pa zaključiše da je u Svetištu imao viđenje. Nastojao im se doduše izraziti znakovima, ali osta nijem.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 Kad se navršiše dani njegove službe, otiđe kući.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 Nakon tih dana zatrudnje Elizabeta, njegova žena. Krila se pet mjeseci govoreći:
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 “Evo, to mi je učinio Gospodin u dane kad mu se svidje skinuti s mene sramotu među ljudima.”
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 U šestome mjesecu posla Bog anđela Gabriela u galilejski grad imenom Nazaret
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 k djevici zaručenoj s mužem koji se zvao Josip iz doma Davidova; a djevica se zvala Marija.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 Anđeo uđe k njoj i reče: “Zdravo, milosti puna! Gospodin s tobom!”
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 Na tu se riječ ona smete i stade razmišljati kakav bi to bio pozdrav.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 No anđeo joj reče: “Ne boj se, Marijo! Ta našla si milost u Boga.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 Evo, začet ćeš i roditi sina i nadjenut ćeš mu ime Isus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 On će biti velik i zvat će se Sin Svevišnjega. Njemu će Gospodin Bog dati prijestolje Davida, oca njegova,
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 i kraljevat će nad domom Jakovljevim uvijeke i njegovu kraljevstvu neće biti kraja.” (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 Nato će Marija anđelu: “Kako će to biti kad ja muža ne poznajem?”
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 Anđeo joj odgovori: “Duh Sveti sići će na te i sila će te Svevišnjega osjeniti. Zato će to čedo i biti sveto, Sin Božji.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 A evo tvoje rođakinje Elizabete: i ona u starosti svojoj zače sina. I njoj, nerotkinjom prozvanoj, ovo je već šesti mjesec.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 Ta Bogu ništa nije nemoguće!”
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 Nato Marija reče: “Evo službenice Gospodnje, neka mi bude po tvojoj riječi!” I anđeo otiđe od nje.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 Tih dana usta Marija i pohiti u Gorje, u grad Judin.
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 Uđe u Zaharijinu kuću i pozdravi Elizabetu.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 Čim Elizabeta začu Marijin pozdrav, zaigra joj čedo u utrobi. I napuni se Elizabeta Duha Svetoga
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 i povika iz svega glasa: “Blagoslovljena ti među ženama i blagoslovljen plod utrobe tvoje!
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 Ta otkuda meni da mi dođe majka Gospodina mojega?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 Gledaj samo! Tek što mi do ušiju doprije glas pozdrava tvojega, zaigra mi od radosti čedo u utrobi.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 Blažena ti što povjerova da će se ispuniti što ti je rečeno od Gospodina!”
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Tada Marija reče: “Veliča duša moja Gospodina,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 klikće duh moj u Bogu, mome Spasitelju,
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 što pogleda na neznatnost službenice svoje: odsad će me, evo, svi naraštaji zvati blaženom.
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 Jer velika mi djela učini Svesilni, sveto je ime njegovo!
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 Od koljena do koljena dobrota je njegova nad onima što se njega boje.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Iskaza snagu mišice svoje, rasprši oholice umišljene.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 Silne zbaci s prijestolja, a uzvisi neznatne.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 Gladne napuni dobrima, a bogate otpusti prazne.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Prihvati Izraela, slugu svoga, kako obeća ocima našim:
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 spomenuti se dobrote svoje prema Abrahamu i potomstvu njegovu dovijeka.” (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 Marija osta s Elizabetom oko tri mjeseca, a onda se vrati kući.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Elizabeti se međutim navršilo vrijeme da rodi. I porodi sina.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 Kad su njezini susjedi i rođaci čuli da joj Gospodin obilno iskaza dobrotu, radovahu se s njome.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 Osmoga se dana okupe da obrežu dječaka. Htjedoše ga prozvati imenom njegova oca - Zaharija,
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 no mati se njegova usprotivi: “Nipošto, nego zvat će se Ivan!”
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 Rekoše joj na to: “Ta nikoga nema od tvoje rodbine koji bi se tako zvao.”
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 Tada znakovima upitaju oca kojim ga imenom želi prozvati.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 On zaiska pločicu i napisa “Ivan mu je ime!” Svi se začude,
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 a njemu se umah otvoriše usta i jezik te progovori blagoslivljajući Boga.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 Strah obuze sve njihove susjede, a po svem su se Gorju judejskom razglašavali svi ti događaji.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 I koji su god čuli, razmišljahu o tome pitajući se: “Što li će biti od ovoga djeteta?” Uistinu, ruka Gospodnja bijaše s njime.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 A Zaharija, otac njegov, napuni se Duha Svetoga i stade prorokovati:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 “Blagoslovljen Gospodin Bog Izraelov, što pohodi i otkupi narod svoj!
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 Podiže nam snagu spasenja u domu Davida, sluge svojega,
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 kao što obeća na usta svetih proroka svojih odvijeka: (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 spasiti nas od neprijatelja naših i od ruke sviju koji nas mrze;
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 iskazati dobrotu ocima našim i sjetiti se svetog Saveza svojega,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 zakletve kojom se zakle Abrahamu, ocu našemu: da će nam dati
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 te mu, izbavljeni iz ruku neprijatelja, služimo bez straha
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 u svetosti i pravednosti pred njim u sve dane svoje.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 A ti, dijete, prorok ćeš se Svevišnjega zvati jer ćeš ići pred Gospodinom da mu pripraviš putove,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 da pružiš spoznaju spasenja narodu njegovu po otpuštenju grijeha njihovih,
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 darom premilosrdnog srca Boga našega po kojem će nas pohoditi Mlado sunce s visine
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 da obasja one što sjede u tmini i sjeni smrtnoj, da upravi noge naše na put mira.”
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 Dječak je međutim rastao i duhom jačao. Boravio je u pustinji sve do dana svoga javnog nastupa pred Izraelom.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.