< Jošua 9 >

1 O tim su događajima čuli svi kraljevi s onu stranu Jordana - u Gorju, u Šefeli i duž čitave obale Velikoga mora sve do Libanona: Hetiti, Amorejci, Kanaanci, Perižani, Hivijci, Jebusejci -
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 pa se svi udružiše da složno udare protiv Jošue i Izraela.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 A stanovnici Gibeona, poučeni onim što Jošua učini Jerihonu i Aju,
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 dosjete se lukavstvu. Uzmu hiniti da su putnici: bace na svoje magarce stare vreće i vinske mješine, poderane i zakrpane.
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 Obuli su na noge rabljenu i pokrpanu obuću i vrgli na se staru odjeću. Sav kruh što su ga ponijeli na put bijaše suh i razdrobljen.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 Stigoše Jošui u gilgalski tabor i rekoše njemu i ljudima Izraelcima: “Dolazimo iz daleke zemlje, sklopite savez s nama.”
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 Ali ljudi Izraelci kažu tim Hivijcima: “Tko zna ne živite li možda među nama? Kako ćemo, dakle, sklopiti savez s vama?”
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 A oni odgovore Jošui: “Tvoje smo sluge!” Jošua ih upita: “Tko ste i odakle dolazite?”
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 Odgovore: “Daleka je zemlja iz koje dolaze tvoje sluge u ime Jahve, Boga tvojega: čuli smo za slavu njegovu i za sve što je učinio u Egiptu
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 i za ono što je učinio dvojici kraljeva amorejskih koji su vladali s onu stranu Jordana - Sihonu, kralju hešbonskom, i Ogu, kralju bašanskom u Aštarotu.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 Tada nam rekoše naše starješine i svi u našoj zemlji: 'Opskrbite se hranom za put, pođite im u susret i recite im: Vaše smo sluge, sklopite dakle savez s nama.'
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 Evo našega kruha: vruć smo ponijeli na put od kuća svojih kada smo krenuli k vama, a sada je, evo, suh i razdrobljen.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 A ovo su vinski mjehovi: nove smo ih nalili, pa su se, evo, već poderali; i haljine naše i obuća već su trošni od dalekog puta.”
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 I povjerovaše im ljudi po putnoj opskrbi, ne pitajući Jahvu što će im reći.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 Jošua uglavi s njima mir i sklopi savez s njima da će ih poštedjeti. I glavari se na to zakunu.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 A poslije tri dana, pošto su sklopili s njima savez, saznalo se da su im susjedi i da žive usred Izraela.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 Tada krenu Izraelci iz tabora i stignu u njihove gradove, a to su bili Gibeon, Kefira, Beerot i Kirjat Jearim.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 Ali ih nisu napali sinovi Izraelovi, jer su im se glavari zajednice zakleli Jahvom, Bogom Izraelovim. Ali sva zajednica poče rogoboriti protiv glavara.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 Tada svi glavari rekoše zajednici: “Mi smo im se zakleli Jahvom, Bogom Izraelovim, i zato ih ne smijemo dirati.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 Evo što ćemo: pustimo ih da žive, kako nas ne bi stigla srdžba zbog zakletve kojom smo se zakleli.”
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 Još dometnuše glavari: “Neka žive i neka budu drvosječe i vodonoše svoj zajednici.” Sva zajednica prihvati što rekoše glavari.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Jošua pozva Gibeonce i reče im: “Zašto nas prevariste govoreći: 'Vrlo smo daleko od vas', kad eto živite usred nas?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Zato će sada na vama biti kletva i nikada neće nestati među vama ropstva: bit ćete drvosječe i vodonoše za Dom Boga moga.”
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 Oni odgovore Jošui: “Sa svih strana dolazili su glasovi nama, slugama tvojim, kako je Jahve, Bog tvoj, odredio Mojsiju, sluzi svomu, da će vam dati svu zemlju i da će istrijebiti ispred vas sve stanovnike ove zemlje; silno smo se uplašili od vas za svoje živote i zato smo učinili ovo.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 I sada smo, evo, u tvojim rukama: učini s nama što misliš da je dobro i pravo.”
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 A on im je učinio ovako: izbavio ih iz ruku sinova Izraelovih te ih nisu pobili.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 I od toga dana naredi im Jošua da sijeku drva i nose vodu, sve do danas, za zajednicu i za žrtvenik Jahvin na mjestu koje se god izabere.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Jošua 9 >