< Ivan 9 >

1 Prolazeći ugleda čovjeka slijepa od rođenja.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 Zapitaše ga njegovi učenici: “Učitelju, tko li sagriješi, on ili njegovi roditelji te se slijep rodio?”
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Odgovori Isus: “Niti sagriješi on niti njegovi roditelji, nego je to zato da se na njemu očituju djela Božja.”
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 “Dok je dan, treba da radimo djela onoga koji me posla. Dolazi noć, kad nitko ne može raditi.
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 Dok sam na svijetu, svjetlost sam svijeta.”
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 To rekavši, pljune na zemlju i od pljuvačke načini kal pa mu kalom premaza oči.
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 I reče mu: “Idi, operi se u kupalištu Siloamu!” - što znači “Poslanik.” Onaj ode, umije se pa se vrati gledajući.
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 Susjedi i oni koji su ga prije viđali kao prosjaka govorili su: “Nije li to onaj koji je sjedio i prosio?”
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Jedni su govorili: “On je.” Drugi opet: “Nije, nego mu je sličan.” On je sam tvrdio: “Da, ja sam!”
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 Nato ga upitaše: “Kako su ti se otvorile oči?”
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 On odgovori: “Čovjek koji se zove Isus načini kal, premaza mi oči i reče mi: 'Idi u Siloam i operi se.' Odoh dakle, oprah se i progledah.”
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 Rekoše mu: “Gdje je on?” Odgovori: “Ne znam.”
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 Tada odvedoše toga bivšeg slijepca farizejima.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 A toga dana kad Isus načini kal i otvori njegove oči, bijaše subota.
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 Farizeji ga počeše iznova ispitivati kako je progledao. On im reče: “Stavio mi kal na oči i ja se oprah - i evo vidim.”
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 Nato neki između farizeja rekoše: “Nije taj čovjek od Boga: ne pazi na subotu.” Drugi su pak govorili: “A kako bi jedan grešnik mogao činiti takva znamenja?” I nastade među njima podvojenost.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 Zatim ponovno upitaju slijepca: “A što ti kažeš o njemu? Otvorio ti je oči!” On odgovori: “Prorok je!”
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 Židovi ipak ne vjerovahu da on bijaše slijep i da je progledao dok ne dozvaše roditelje toga koji je progledao
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 i upitaše ih: “Je li ovo vaš sin za kojega tvrdite da se slijep rodio? Kako sada vidi?”
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 Njegovi roditelji odvrate: “Znamo da je ovo naš sin i da se slijep rodio.
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 A kako sada vidi, to mi ne znamo; i tko mu je otvorio oči, ne znamo. Njega pitajte! Punoljetan je: neka sam o sebi govori!”
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 Rekoše tako njegovi roditelji jer su se bojali Židova. Židovi se doista već bijahu dogovorili da se iz sinagoge ima izopćiti svaki koji njega prizna Kristom.
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 Zbog toga rekoše njegovi roditelji: “Punoljetan je, njega pitajte!”
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 Pozvaše stoga po drugi put čovjeka koji bijaše slijep i rekoše mu: “Podaj slavu Bogu! Mi znamo da je taj čovjek grešnik!”
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 Nato im on odgovori: “Je li grešnik, ja ne znam. Jedno znam: slijep sam bio, a sada vidim.”
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 Rekoše mu opet: “Što ti učini? Kako ti otvori oči?”
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 Odgovori im: “Već vam rekoh i ne poslušaste me. Što opet hoćete čuti? Da ne kanite i vi postati njegovim učenicima?”
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 Nato ga oni izgrdiše i rekoše: “Ti si njegov učenik, a mi smo učenici Mojsijevi.
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 Mi znamo da je Mojsiju govorio Bog, a za ovoga ne znamo ni odakle je.”
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 Odgovori im čovjek: “Pa to i jest čudnovato da vi ne znate odakle je, a meni je otvorio oči.
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 Znamo da Bog grešnike ne uslišava; nego je li tko bogobojazan i vrši li njegovu volju, toga uslišava.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Odvijeka se nije čulo da bi tko otvorio oči slijepcu od rođenja. (aiōn g165)
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn g165)
33 Kad ovaj ne bi bio od Boga, ne bi mogao činiti ništa”.
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 Odgovore mu: “Sav si se u grijesima rodio, i ti nas da učiš?” i izbaciše ga.
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Dočuo Isus da su onoga izbacili pa ga nađe i reče mu: “Ti vjeruješ u Sina Čovječjega?”
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 On odgovori: “A tko je taj, Gospodine, da vjerujem u njega?”
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 Reče mu Isus: “Vidio si ga! To je onaj koji govori s tobom!”
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 A on reče: “Vjerujem, Gospodine!” I baci se ničice preda nj.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Tada Isus reče: “Radi suda dođoh na ovaj svijet: da progledaju koji ne vide, a koji vide, da oslijepe!”
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 Čuli to neki od farizeja koji su bili s njime pa ga upitaju: “Zar smo i mi slijepi?”
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Isus im odgovori: “Da ste slijepi, ne biste imali grijeha. No vi govorite: 'Vidimo' pa grijeh vaš ostaje.”
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.

< Ivan 9 >