< Job 33 >
1 Čuj dakle, Jobe, što ću ti kazati, prikloni uho mojim besjedama.
“Amma yanzu, Ayuba, ka saurari abin da zan ce; ka sa hankali ga kowane abin da zan faɗa.
2 Evo, usta sam svoja otvorio, a jezik riječi pod nepcem mi stvara.
Zan yi magana; kalmomina suna dab da fitowa daga bakina.
3 Iskreno će ti zborit' srce moje, usne će čistu izreći istinu.
Abin da zan faɗa gaskiya ne daga cikin zuciyata; bakina zai faɗi gaskiyar abin da na sani.
4 TÓa i mene je duh Božji stvorio, dah Svesilnoga oživio mene.
Ruhun Allah ne ya yi ni; numfashin Maɗaukaki ya ba ni rai.
5 Ako uzmogneš, ti me opovrgni; spremi se da se suprotstaviš meni!
Ka amsa mini in za ka iya; ka yi shirin fuskanta ta.
6 Gle, kao i ti, i ja sam pred Bogom, kao i ti, od gline bjeh načinjen;
Ni kamar ka nake a gaban Allah; ni ma daga ƙasa aka yi ni.
7 zato ja strahom tebe motrit' neću, ruka te moja neće pritisnuti.
Kada ka ji tsorona, ba abin da zai fi ƙarfinka.
8 Dakle, na moje uši rekao si - posve sam jasno tvoje čuo riječi:
“Amma ka faɗa na ji, na ji daidai abin da ka faɗa,
9 'Nedužan sam i bez ikakva grijeha; prav sam i nema krivice na meni.
‘ni mai tsarki ne marar zunubi; ina da tsabta kuma ba ni da laifi.
10 Al' On izlike protiv mene traži i za svojeg me drži dušmanina.
Duk da haka Allah ya same ni da laifi; ya ɗauke ni maƙiyinsa,
11 Noge je moje u klade metnuo, nad svakim mojim on pazi korakom.'
ya daure ƙafafuna da sarƙa; yana tsaron duk inda na bi.’
12 Ovdje, kažem ti, u pravu ti nisi, jer s Bogom čovjek mjerit' se ne može.
“Amma na gaya maka, a nan ba ka yi daidai ba, gama Allah ya fi mutum girma.
13 Pa zašto s njime zamećeš prepirku što ti na svaku riječ ne odgovara?
Don me ka yi masa gunaguni cewa ba ya amsa tambayoyin mutum?
14 Bog zbori nama jednom i dva puta, al' čovjek na to pažnju ne obraća.
Gama Allah yana magana, yanzu ga wannan hanya, yanzu kuma ga wata hanya ko da yake ba lalle mutum yă lura ba.
15 U snovima, u viđenjima noćnim, kada san dubok ovlada ljudima i na ležaju dok tvrdo snivaju,
A cikin mafarki, cikin wahayi da dare, sa’ad da barci mai zurfi ya fāɗo a kan mutane lokacin da suke cikin barci kan gadajensu,
16 tad on govori na uho čovjeku i utvarama plaši ga jezivim
mai yiwuwa yă yi musu magana a cikin kunnuwansu yă razana su da gargaɗinsa,
17 da ga od djela njegovih odvrati, da u čovjeku obori oholost,
don a juyar da su daga abin da yake yi da ba daidai ba a kuma hana su daga girman kai,
18 da dušu njegovu spasi od jame i život mu od puta u Podzemlje.
don a kāre su daga fāɗuwa cikin rami, a kāre su daga hallaka ta wurin takobi.
19 Bolešću on ga kara na ležaju kad mu se kosti tresu bez prestanka,
“Ko kuma mutum yă sha horo ta wurin kwanciya da ciwo da rashin jin daɗi cikin ƙasusuwansa,
20 kad se kruh gadi njegovu životu i ponajbolje jelo duši njegovoj;
yadda zai ji ƙyamar abinci, har yă ƙi son abinci mafi daɗi.
21 kada mu tijelo gine naočigled i vide mu se kosti ogoljele,
Naman jikinsa ya lalace ba wani abu mai kyau a ciki kuma ƙasusuwansa da suke a rufe da tsoka yanzu duk sun fito.
22 kad mu se duša približava jami a život njegov boravištu mrtvih.
Ransa yana matsawa kusa da rami, ransa kuma kusa da’yan aikan mutuwa.
23 Ako se uza nj nađe tad anđeo, posrednik jedan između tisuću, da čovjeka na dužnost opomene,
Duk da haka, in akwai mala’ika a gefensa kamar matsakanci, ɗaya daga cikin dubu, da zai gaya wa mutum abin da yake daidai gare shi,
24 pa se sažali nad njim i pomoli: 'Izbavi ga da u jamu ne ide; za život njegov nađoh otkupninu!
yă yi masa alheri yă ce, ‘Kada ka bari yă fāɗa cikin rami, na samu fansa dominsa.’
25 Neka mu tijelo procvate mladošću, nek' se vrati u dane mladenačke!'
Sa’an nan fatar jikinsa za tă zama sabuwa kamar ta jariri; za tă zama kamar lokacin da yake matashi.
26 Vapije k Bogu i Bog ga usliša: radosno On ga pogleda u lice; vrati čovjeku pravednost njegovu.
Ya yi addu’a ga Allah ya kuwa samu alheri a wurinsa, yana ganin fuskar Allah yana kuma yin sowa don murna; Allah ya mayar da shi ya zama mai adalci.
27 Tada čovjek pred ljudima zapjeva: 'Griješio sam i pravo izvrtao, ali mi Bog zlom nije uzvratio.
Sa’an nan sai ya zo wurin, wurin mutane ya ce, ‘Na yi zunubi, na kauce wa abin da yake daidai, amma ban samu abin da ya kamata in samu ba.
28 On mi je dušu spasio od jame i život mi se veseli svjetlosti.'
Ya fanshi raina daga fāɗawa cikin rami, kuma zan rayu in ji daɗin hasken.’
29 Gle, sve to Bog je spreman učiniti do dva i do tri puta za čovjeka:
“Allah ya yi wa mutum duk waɗannan, sau biyu, har ma sau uku.
30 da dušu njegovu spasi od jame i da mu život svjetlošću obasja.
Ya juyo da ransa daga fāɗawa cikin rami, don hasken rai ya haskaka a kansa.
31 Pazi dÓe, Jobe, dobro me poslušaj; šuti, jer nisam sve još izrekao.
“Ka sa hankali da kyau, Ayuba, ka saurare ni; ka yi shiru zan yi magana.
32 Ako riječi još imaš, odvrati mi, zbori - rado bih opravdao tebe.
In kana da abin da za ka ce, ka amsa mini; yi magana, domin ina so in’yantar da kai.
33 Ako li nemaš, poslušaj me samo: pazi, rad bih te poučit' mudrosti.”
Amma in ba haka ba, sai ka saurare ni; yi shiru, zan kuma koya maka hikima.”