< Job 31 >
1 Sa svojim očima savez sam sklopio da pogledat neću nijednu djevicu.
“Na yi alkawari da idanuna kada su dubi budurwa da muguwar sha’awa.
2 A što mi je Bog odozgo dosudio, kakva mi je baština od Svesilnoga?
Gama mene ne rabon mutum daga Allah a sama, gādonsa daga Maɗaukaki a sama?
3 TÓa nije li nesreća za opakoga, a nevolja za one koji zlo čine?
Ba masifa ba ne domin mugaye, hallaka kuma ga waɗanda suka yi ba daidai ba?
4 Ne proniče li on sve moje putove, ne prebraja li on sve moje korake?
Bai ga hanyoyina ba ne bai ƙirga kowace takawata ba?
5 Zar sam ikad u društvu laži hodio, zar mi je noga k prijevari hitjela?
“In da na yi tafiya cikin rashin gaskiya ko kuma ƙafata ta yi sauri zuwa yin ƙarya,
6 Nek' me na ispravnoj mjeri Bog izmjeri pa će uvidjeti neporočnost moju!
Bari Allah yă auna a kan ma’auni na gaskiya zai kuma san cewa ni marar laifi ne.
7 Ako mi je korak s puta kad zašao, ako mi se srce za okom povelo, ako mi je ljaga ruke okaljala,
In takawata ta kauce daga hanya, in zuciyata ta bi abin da idanuna ke so, ko kuma in hannuwana suna da laifi;
8 neka drugi jede što sam posijao, neka sve moje iskorijene izdanke!
bari waɗansu su ci abin da na shuka, kuma bari a tuge amfanin gonata.
9 Ako mi zavede srce žena neka, ako za vratima svog bližnjeg kad vrebah,
“In sha’awar mace ya shiga mini zuciya, ko kuma na laɓe a ƙofar maƙwabcina,
10 neka moja žena drugom mlin okreće, neka s drugim svoju podijeli postelju!
sai matata ta niƙa hatsin wani kuma waɗansu maza su kwana da ita.
11 Djelo bestidno time bih počinio, zločin kojem pravda treba da presudi,
Gama wannan zai zama abin kunya, zunubin da za a yi shari’a a kai.
12 užego vatru što žeže do Propasti i što bi svu moju sažgala ljetinu.
Wuta ce take ƙuna har ta hallakar; za tă cinye saiwar abin da na shuka ƙurmus.
13 Ako kada prezreh pravo sluge svoga il' služavke, sa mnom kad su se parbili,
“In da na danne wa bayina maza da mata hakkinsu, sa’ad da suke da damuwa da ni,
14 što ću učiniti kada Bog ustane? Što ću odvratit' kad račun zatraži?
me zan yi lokacin da Allah ya tuhume ni? Me zan ce lokacin da ya tambaye ni?
15 Zar nas oba on ne stvori u utrobi i jednako sazda u krilu majčinu?
Shi wanda ya yi ni a cikin uwata ba shi ne ya yi su ba? Ba shi ne ya yi mu a cikin uwayenmu ba?
16 Ogluših li se na molbe siromaha ili rasplakah oči udovičine?
“In na hana wa matalauta abin da suke so, ko kuma in sa idanun gwauruwa su yi nauyi don kuka,
17 Jesam li kada sam svoj jeo zalogaj a da ga nisam sa sirotom dijelio?
in na ajiye burodina don kaina kaɗai, ban kuwa ba wa marayu abinci sa’ad da suke jin yunwa,
18 TÓa od mladosti k'o otac sam mu bio, vodio sam ga od krila materina!
amma tun suna tasowa na lura da su, kamar yadda mahaifi zai lura da ɗa, kuma tun da aka haife ni ina lura da gwauruwa.
19 Zar sam beskućnika vidio bez odjeće ili siromaha kog bez pokrivača
In da na ga wani yana mutuwa don rashin sutura, ko wani mai bukata da ba shi da riga,
20 a da mu bedra ne blagosloviše mene kad se runom mojih ovaca ogrija?
kuma zuciyarsa ba tă gode mini ba don na yi masa sutura da gashin tumakina,
21 Ako sam ruku na nevina podigao znajuć' da mi je na vratima branitelj,
in na ɗaga hannuna don in cuci maraya, domin na san in na faɗa za a ji ni a wurin masu shari’a,
22 nek' se rame moje od pleća odvali i neka mi ruka od lakta otpadne!
bari hannuna yă guntule daga kafaɗata, bari yă tsinke daga inda aka haɗa shi.
23 Jer strahote Božje na mene bi pale, njegovu ne bih odolio veličanstvu.
Gama ina jin tsoron hallaka daga Allah, kuma domin tsoron ɗaukakarsa ba zan iya yin waɗannan abubuwa ba.
24 Zar sam u zlato pouzdanje stavio i rekao zlatu: 'Sigurnosti moja!'
“In na dogara ga zinariya ko kuma na ce wa zallan zinariya, ‘Gare ki nake dogara,’
25 Zar sam se veliku blagu radovao, bogatstvima koja su mi stekle ruke?
in na yi fahariya don yawan dukiyata, arzikin da hannuwana suka samu.
26 Zar se, gledajući sunce kako blista i kako mjesec sjajni nebom putuje,
In na dubi rana cikin haskenta, ko kuma wata yana tafiyarsa,
27 moje srce dalo potajno zavesti da bih rukom njima poljubac poslao?
zuciyata ta jarrabtu gare su a ɓoye, hannuna kuma ya sumbace su.
28 Grijeh bi to bio što za sudom vapije, jer Boga višnjega bih se odrekao.
Waɗannan ma za su zama zunubin da za a shari’anta ke nan don zai zama na yi wa Allah na sama rashin aminci.
29 Zar se obradovah nevolji dušmana i likovah kad ga je zlo zadesilo,
“In na yi murna domin mugun abu ya faru da maƙiyina; ko kuma domin wahala ta same shi,
30 ja koji ne dadoh griješiti jeziku, proklinjući ga i želeći da umre?
ban bar bakina yă yi zunubi ta wurin la’anta shi ba,
31 Ne govorahu li ljudi mog šatora: 'TÓa koga nije on mesom nasitio'?
in mutanen gidana ba su taɓa cewa, ‘Wane ne bai ƙoshi da naman Ayuba ba?’
32 Nikad nije stranac vani noćivao, putniku sam svoja otvarao vrata.
Ba baƙon da ya taɓa kwana a titi, gama koyaushe ƙofata tana buɗe domin matafiya,
33 Zar sam grijehe svoje ljudima tajio, zar sam u grudima skrivao krivicu
in na ɓoye zunubina yadda mutane suke yi, ta wurin ɓoye laifina a cikin zuciyata,
34 jer sam se plašio govorkanja mnoštva i strahovao od prezira plemenskog te sam mučao ne prelazeć' svoga praga?
domin ina tsoron taron mutane kuma ina tsoron wulaƙancin da dangina za su yi mini, sai na yi shiru kuma ban fita waje ba.
35 O, kad bi koga bilo da mene sasluša! Posljednju sam svoju riječ ja izrekao: na Svesilnom je sad da mi odgovori! Nek' mi optužnicu napiše protivnik,
(“Kash, da ina da wanda zai ji ni! Na sa hannu ga abin da na faɗa don kāre kaina, bari Maɗaukaki yă amsa mini; bari mai tuhumata da laifi yă yi ƙarata a rubuce.
36 i ja ću je nosit' na svome ramenu, čelo ću njome k'o krunom uresit'.
Ba shakka sai in ɗora a kafaɗata, zan aza a kaina kamar rawani.
37 Dat ću mu račun o svojim koracima i poput kneza pred njega ću stupiti.”
Zan ba shi lissafin duk abin da na taɓa yi; zan zo gabansa kamar ɗan sarki.)
38 Ako je na me zemlja moja vikala, ako su s njom brazde njezine plakale;
“In ƙasata tana kuka da ni kunyoyinta duk sun cika da hawaye,
39 ako sam plodove jeo ne plativši i ako sam joj ojadio ratare,
in na kwashe amfaninta ban biya ba ko kuma na kashe masu ita,
40 [40a] neka mjesto žita po njoj niče korov, a mjesto ječma nek' posvud kukolj raste! [40b] Konac riječi Jobovih.
bari ƙaya ta fito a maimakon alkama ciyawa kuma a maimakon sha’ir.” Maganar Ayuba ta ƙare.