< Job 28 >

1 “Da, srebro ima svoja nalazišta, a zlato mjesta gdje se pročišćava.
Akwai ramin azurfa akwai kuma wurin da ake tace zinariya.
2 Ruda željezna iz zemlje se vadi, a iz rudače rastaljene bakar.
Daga cikin ƙasa ake ciro ƙarfe, ana kuma narkar da tagulla daga cikin dutse.
3 Ljudi tami postavljaju granice i kopaju do najvećih dubina za kamenom u mraku zakopanim.
Mutum ya kawo ƙarshen duhu; yakan bincike zuzzurfar iyaka, yana neman duwatsu a wuri mafi duhu.
4 Čeljad iz tuđine rovove dube do kojih ljudska ne dopire noga, visi njišuć' se, daleko od ljudi.
Nesa da inda mutane suke zama, yakan huda rami yă yi abin lilo, a wurin da mutane ba sa bi.
5 Krilo zemlje iz kojeg kruh nam niče kao od vatre sve je razrovano.
Cikin ƙasa inda ake samun abinci, a ƙarƙashinta kuwa zafi ne kamar wuta;
6 Stijene njene safira su skrovišta, prašina zlatna krije se u njima.
akwai duwatsu masu daraja a cikin duwatsunta, akwai kuma zinariya a cikin ƙurarta.
7 Tih putova ne znaju grabljivice, jastrebovo ih oko ne opaža.
Tsuntsu mai farauta bai san hanyarta ba, ba shahon da ya taɓa ganin ta.
8 Zvijeri divlje njima nisu kročile niti je kada lav njima prošao.
Manyan namun jeji ba su taɓa binta ba, ba zakin da ya taɓa binta.
9 Ali na kamen diže čovjek ruku te iz korijena prevraća planine.
Hannun mutum ya iya sarrafa ƙanƙarar duwatsu, yă kuma tumɓuke tushen duwatsu.
10 U kamenu prokopava prolaze, oko mu sve dragocjeno opaža.
Yana tona rami a cikin duwatsu idanunsa suna ganin dukan dukiyar da ke cikin duwatsun.
11 Žilama vode on tok zaustavlja; stvari skrivene nosi na vidjelo.
Yana nema daga ina ruwan rafi yake ɓulɓulowa yana kuma binciko abubuwan da suke a ɓoye yă kawo su cikin haske.
12 Ali otkuda nam Mudrost dolazi? Na kojemu mjestu Razum prebiva?
Amma a ina ne za a iya samun hikima? Ina fahimta take zama?
13 Čovjek njezina ne poznaje puta, u zemlji živih nisu je otkrili.
Mutum bai gane muhimmancinta ba, ba a samunta a ƙasar masu rai.
14 Bezdan govori: 'U meni je nema!' a more: 'Ne nalazi se kod mene!'
Zurfi ya ce, “Ba ta wurina”; teku ya ce, “Ba ta wurina.”
15 Zlatom se čistim kupiti ne može, ni cijenu njenu srebrom odmjeriti;
Ba irin zinariyar da za tă iya sayenta, ko kuma a iya auna nauyinta da azurfa.
16 ne mjeri se ona zlatom ofirskim, ni oniksom skupim pa ni safirom.
Ba za a iya sayenta da zinariyar Ofir, ko sauran duwatsu masu daraja ba.
17 Sa zlatom, staklom ne poređuje se, nit' se daje za sud od suha zlata.
Zinariya da madubi ba za su iya gwada kansu da ita ba, ba kuwa za a iya musayarta da abubuwan da aka yi da zinariya ba.
18 Čemu spominjat' prozirac, koralje, bolje je steći Mudrost no biserje.
Kada ma a ce murjani da duwatsu masu walƙiya; farashin hikima ya fi na lu’ulu’ai.
19 Što je prema njoj topaz etiopski? Ni čistim zlatom ne procjenjuje se.
Ba za a iya daidaita darajarta da duwatsun Tofaz na Kush ba, zallar zinariya ma ba tă isa ta saye ta ba.
20 Ali otkuda nam Mudrost dolazi? Na kojemu mjestu Razum prebiva?
“To, daga ina ke nan hikima ta fito? Ina fahimta take zama?
21 Sakrivena je očima svih živih; ona izmiče pticama nebeskim.
An ɓoye ta daga idanun kowane abu mai rai, har tsuntsayen sararin sama ma an ɓoye masu ita.
22 Propast paklena i Smrt izjavljuju: 'Za slavu njenu mi smo samo čuli.' (questioned)
Hallaka da mutuwa suna cewa, ‘Jita-jitarta kaɗai muke ji.’
23 Jedino je Bog put njen proniknuo, on jedini znade gdje se nalazi.
Allah ya gane hanyar zuwa wurinta. Shi ne kaɗai ya san inda take zama,
24 Jer pogledom granice zemlje hvata i opaža sve pod svodom nebeskim.
Gama yana ganin iyakar duniya kuma yana ganin duk abin da yake ƙarƙashin sama.
25 Kad htjede vjetru odredit težinu i mjerilom svu vodu izmjeriti,
Lokacin da ya yi iska ya sa ta hura, ya kuma auna ruwaye.
26 kad je zakone daždu nametnuo i oblacima gromovnim putove,
Lokacin da ya yi wa ruwan sama doka da kuma hanya domin walƙiya,
27 tad ju je vidio te izmjerio, učvrstio i do dna ispitao.
sai ya dubi hikima ya auna ta; ya tabbatar da ita, ya gwada ta.
28 A potom je rekao čovjeku: Strah Gospodnji - eto što je mudrost; 'Zla se kloni' - to ti je razumnost.”
Ya kuma ce wa mutum, ‘Tsoron Ubangiji shi ne hikima, kuma guje wa mugunta shi ne fahimi.’”

< Job 28 >