< Job 20 >
1 Sofar iz Naamata progovori tad i reče:
Sai Zofar mutumin Na’ama ya amsa,
2 “Misli me tjeraju da ti odgovorim, i zato u meni vri to uzbuđenje
“Tunanin da ya dame ni ya sa dole in amsa domin abin ya dame ni sosai.
3 dok slušam ukore koji me sramote, al' odgovor mudar um će moj već naći.
Na ji wani zargin da ka yi mini na reni, kuma yadda na gane, shi ya sa zan ba da amsa.
4 Zar tebi nije od davnine poznato, otkad je čovjek na zemlju stavljen bio,
“Ba shakka ka san yadda abin yake tuntuni, tun da aka sa mutum cikin duniya,
5 da je kratka vijeka radost opakoga, da kao tren prođe sreća bezbožnička.
mugun mutum bai taɓa daɗewa ba, farin cikin mutum na ɗan gajeren lokaci ne.
6 Pa ako stasom i do neba naraste, ako mu se glava dotakne oblaka,
Ko da ya ƙasaita ya kai sararin sama, kansa kuma yana taɓa gizagizai.
7 poput utvare on zauvijek nestaje; koji ga vidješe kažu: 'Gdje je sad on?'
Zai hallaka har abada, kamar bayan gidansa; waɗanda suka gan shi za su ce, ‘Ina yake?’
8 Kao san bez traga on se rasplinjuje, nestaje ga kao priviđenja noćnog.
Kamar mafarki haka zai ɓace, ba za a ƙara ganinsa ba zai ɓace kamar wahayi da dare.
9 Nijedno ga oko više gledat neće, niti će ga mjesto njegovo vidjeti
Idon da ya gan shi ba zai ƙara ganinsa ba; wurin zamansa ba zai sāke ganinsa ba.
10 Njegovu će djecu gonit' siromasi: rukama će svojim vraćati oteto.
Dole’ya’yansa su mayar wa matalauta abin da ya kamata; dole hannuwansa su mayar da dukiyarsa.
11 Kosti su njegove bujale mladošću; gle, zajedno s njome pokošen je sada.
Jin ƙarfi da ya cika ƙasusuwansa zai kwantar da shi a cikin ƙura.
12 Zlo bijaše slatko njegovim ustima te ga je pod svojim jezikom skrivao;
“Ko da yake mugunta tana da daɗi a bakinsa kuma yana ɓoye ta a harshensa,
13 sladio se pazeć' da ga ne proguta i pod nepcem svojim zadržavao ga.
ko da yake ba zai iya rabuwa da ita ba, yana kuma ajiye ta a bakinsa,
14 Ali hrana ta mu trune u utrobi, otrovom zmijskim u crijevima postaje.
duk da haka abincin da ya ci zai zama da tsami a cikin cikinsa; zai zama kamar dafin maciji a cikinsa.
15 Blago progutano mora izbljuvati. Bog će ga istjerat' njemu iz utrobe.
Zai haras da dukiyar da ya haɗiye; Allah zai sa cikinsa yă haras da su.
16 Iz zmijine glave otrov je sisao: sada umire od jezika gujina.
Zai sha dafin maciji; sarar maciji mai dafi za tă tashe shi.
17 Potoke ulja on gledat' više neće, ni vidjet' gdje rijekom med i mlijeko teku.
Ba zai ji daɗin koguna da rafuffuka masu kwarara da zuma da madara ba.
18 Vratit će dobitak ne okusivši ga, neće uživat' u plodu trgovine.
Dole yă ba da abin da ya yi gumi kafin yă samu, ba zai ci ba; ba zai ji daɗin ribar da ya samu daga kasuwancinsa ba.
19 Jer je sirotinju gnjeo i tlačio, otimao kuće koje ne sazida,
Gama ya ci zalin talakawa ya bar su cikin wahala; ya ƙwace gidajen da ba shi ya gina ba.
20 jer ne bješe kraja požudi njegovoj, njegova ga blaga neće izbaviti.
“Ba shakka ba zai samu abin da yake ƙoƙarin samu ba, dukiyarsa ba za tă cece shi ba.
21 Jer mu proždrljivost ništa ne poštedi, ni sreća njegova dugo trajat neće.
Ba abin da ya ragu da zai ɗauka; arzikinsa ba zai dawwama ba.
22 Sred izobilja u škripcu će se naći, svom će snagom na nj se oboriti bijeda.
Yana cikin samun arziki, ɓacin rai zai auka masa; ƙunci mai ƙarfi zai zo masa.
23 I dok hranom bude trbuh svoj punio, Bog će na nj pustiti jarost svoga gnjeva, sasut' dažd strelica na meso njegovo.
Lokacin da ya cika cikinsa, Allah zai zuba fushinsa a kansa, zai daddaka shi.
24 Ako i izmakne gvozdenom oružju, luk će mjedeni njega prostrijeliti.
Ko da yake yana guje wa makamin ƙarfe, kibiya mai bakin tagulla za tă huda shi.
25 Strijelu bi izvuk'o, al' mu probi leđa, a šiljak blistavi viri mu iz žuči. Kamo god krenuo, strepnje ga vrebaju,
Zai zāre ta daga bayansa, tsinin zai fita daga hantarsa; tsoro zai cika shi;
26 na njega tmine sve tajom očekuju. Vatra ga ništi, ni od kog zapaljena, i proždire sve pod njegovim šatorom.
duhu kawai yake jiran dukiyarsa. Wutar da ba a fifita ba za tă cinye shi ta kuma ƙona duk abin da ya rage a tentinsa.
27 Gle, nebo krivicu njegovu otkriva i čitava zemlja na njega se diže.
Sammai za su fallasa laifinsa; duniya za tă yi gāba da shi.
28 Njegovu će kuću raznijeti poplava, otplaviti je u dan Božje jarosti.
Ambaliyar ruwa za tă tafi da gidansa, ruwaye masu gudu a ranar fushin Allah.
29 Takvu sudbinu Bog priprema zlikovcu i takvu baštinu on mu dosuđuje.”
Abin da Allah zai sa yă faru da mugu ke nan, gādon da Allah ya ba shi ke nan.”