< Job 19 >
2 “TÓa dokle ćete mučit' dušu moju, dokle ćete me riječima satirat'?
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 Već deseti put pogrdiste mene i stid vas nije što me zlostavljate.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Pa ako sam zastranio doista, na meni moja zabluda ostaje.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 Mislite li da ste me nadjačali i krivnju moju da ste dokazali?
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Znajte: Bog je to mene pritisnuo i svojom me je on stegnuo mrežom.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Vičem: 'Nasilje!' - nema odgovora; vapijem - ali za me pravde nema.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 Sa svih strana put mi je zagradio, sve staze moje u tminu zavio.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 Slavu je moju sa mene skinuo, sa moje glave strgnuo je krunu.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 Podsijeca me odasvud te nestajem; k'o drvo, nadu mi je iščupao.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 Raspalio se gnjev njegov na mene i svojim me drži neprijateljem.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 U bojnom redu pristižu mu čete, putove proti meni nasipaju, odasvud moj opkoljavaju šator.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 Od mene su se udaljila braća, otuđili se moji poznanici.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 Nestade bližnjih mojih i znanaca, gosti doma mog zaboraviše me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 Sluškinjama sam svojim kao stranac, neznanac sam u njihovim očima.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 Slugu zovnem, a on ne odgovara i za milost ga moram zaklinjati.
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 Mojoj je ženi dah moj omrznuo, gadim se djeci vlastite utrobe.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 I deranima na prezir tek služim, ako se dignem, rugaju se meni.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 Pouzdanicima sam svojim mrzak, protiv mene su oni koje ljubljah.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 Kosti mi se za kožu prilijepiše, osta mi jedva koža oko zuba.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Smilujte mi se, prijatelji moji, jer Božja me je ruka udarila.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Zašto da me k'o Bog sam progonite, zar se niste moga nasitili mesa?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 O, kad bi se riječi moje zapisale i kad bi se u mjed tvrdu urezale;
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 kad bi se željeznim dlijetom i olovom u spomen vječan u stijenu uklesale!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 Ja znadem dobro: moj Izbavitelj živi i posljednji će on nad zemljom ustati.
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 A kad se probudim, k sebi će me dići: iz svoje ću puti tad vidjeti Boga.
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 Njega ja ću kao svojega gledati, i očima mojim neće biti stranac: za njime srce mi čezne u grudima.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 Kad kažete: 'Kako ćemo ga goniti? Koji ćemo razlog protiv njega naći?',
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 mača tad se bojte: grijehu mač je kazna. Saznat ćete tada da imade suda!”
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”