< Jeremija 41 >

1 Ali u sedmom mjesecu dođe Jišmael, sin Elišamina sina Netanije, roda kraljevskoga, sa deset ljudi i potraži Gedaliju, sina Ahikamova, u Mispi. I dok su se ondje, u Mispi, zajedno gostili,
A wata na goma sha bakwai sai Ishmayel ɗan Netaniya, ɗan Elishama, wanda yake mai jinin sarauta yake kuma ɗaya daga cikin hafsoshin sarki, ya zo tare da mutum goma wurin Gedaliya ɗan Ahikam a Mizfa. Yayinda suke ci tare a can,
2 diže se Jišmael, sin Netanijin, sa svojom desetoricom i mačem smakoše Gedaliju, sina Ahikamova. I tako ubi čovjeka koga kralj babilonski bijaše postavio nad zemljom.
sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutum goma waɗanda suke tare da shi suka kashe Gedaliya ɗan Ahikam, ɗan Shafan, da takobi, suka kashe wannan da sarkin Babilon ya naɗa a matsayin gwamna a kan ƙasar.
3 A i sve Judejce koji bijahu s njim u Mispi, i Kaldejce, vojnike što se tu nađoše - Jišmael dade pogubiti.
Ishmayel ya kuma kashe dukan Yahudawan da suke tare da Gedaliya a Mizfa, haka ma ya yi da sojojin Babiloniyawan da suke can.
4 Sutradan, pošto Gedalija bi ubijen, dok još nitko nije znao što se zbilo,
Kashegari bayan an kashe Gedaliya, kafin wani ya san abin da ya faru,
5 dođoše ljudi iz Šekema, Šila i Samarije, njih osamdeset, obrijane brade, poderanih haljina i s urezima po tijelu, noseći u rukama prinose i tamjan da ih prinesu u Domu Jahvinu.
sai ga mutane tamanin daga Shekem, Shilo da Samariya suka zo da gemunsu a aske, da tufafinsu a kece, da jikunansu a tsage, suka kawo hadayun gari da turare tare da su a gidan Ubangiji.
6 Jišmael, sin Netanijin, iziđe im iz Mispe u susret, dok su oni, plačući, išli svojim putem. Kad ih stiže, reče im: “Dođite Gedaliji, sinu Ahikamovu!”
Ishmayel ɗan Netaniya ya fito daga Mizfa don yă sadu da su. Sa’ad da ya sadu da su, sai ya ce, “Ku zo wurin Gedaliya ɗan Ahikam.”
7 A kad stigoše usred grada, Jišmael, sin Netanijin, i njegovi ljudi poklaše ih i baciše u čatrnju.
Da suka shiga cikin birni, sai Ishmayel ɗan Netaniya da mutanen da suke tare da shi suka karkashe su suka zubar a rijiya.
8 A među njima bijaše deset ljudi koji rekoše Jišmaelu: “Nemoj nas ubiti, jer imamo u poljima zakopanih zaliha pšenice, ječma, ulja i meda.” On tada odusta i ne ubi ih s braćom njihovom.
Amma goma daga cikinsu suka ce wa Ishmayel, “Kada ka kashe mu, muna da alkama da sha’ir, mai da kuma zuma, a ɓoye a gona.” Saboda haka ka bar mu kada ka kashe mu tare da sauran.
9 A čatrnja u koju je Jišmael pobacao sva tjelesa pobijenih ljudi, velika čatrnja, bijaše ona ista koju je kralj Asa načinio protiv Baše, kralja izraelskoga. I sad ju je Jišmael, sin Netanijin, napunio pobijenim ljudima.
To, rijiyar da ya zubar da gawawwakin mutanen da ya kashe tare da ta Gedaliya ita ce wadda Sarki Asa ya haƙa a matsayin kāriya saboda Ba’asha sarkin Isra’ila. Ishmayel ɗan Netaniya ya cika ta da gawawwaki.
10 Tada Jišmael odvede ostatak naroda iz Mispe, zajedno s kćerima kraljevim koje je Nebuzaradan, zapovjednik tjelesne straže, povjerio Gedaliji, sinu Ahikamovu: u cik zore krenu Jišmael, sin Netanijin, i zaputi se da prijeđe u zemlju Amonovih sinova.
Ishmayel ya mai da dukan sauran mutanen da suke Mizfa bayi’ya’yan sarki mata tare da dukan sauran da aka bari a can, waɗanda Nebuzaradan shugaban matsaran sarki ya bari a hannun Gedaliya ɗan Ahikam. Ishmayel ɗan Netaniya ya kwashe su ganima, ya tashi don yă haye zuwa wurin Ammonawa.
11 Ali kad Johanan, sin Kareahov, i svi vojni zapovjednici koji bijahu s njim saznadoše za sva zlodjela što ih Jišmael, sin Netanijin, bijaše počinio,
Sa’ad da Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka ji dukan laifofin da Ishmayel ɗan Netaniya ya aikata,
12 uzeše sve svoje vojnike te krenuše u boj na Jišmaela, sina Netanijina. Nađoše ga uz veliku vodu u Gibeonu.
sai suka kwashe dukan mutanensu suka tafi don su yaƙi Ishmayel ɗan Netaniya. Suka iske shi kusa da babban tafki a Gibeyon.
13 Čim oni ljudi što bijahu kod Jišmaela ugledaše Johanana, sina Kareahova, i sve vojne zapovjednike koji bijahu s njime, obradovaše se,
Sa’ad da dukan mutanen da suke tare da Ishmayel suka ga Yohanan ɗan Kareya da shugabannin sojojin da suke tare da shi, sai suka yi farin ciki.
14 i sav narod što ga je Jišmael odveo iz Mispe okrenu se i potrča Johananu, sinu Kareahovu.
Dukan mutanen da Ishmayel ya kame a Mizfa suka juya, suka tafi wurin Yohanan ɗan Kareya.
15 Ali Jišmael, sin Netanijin, sa osam ljudi, pobježe od Johanana i ode k sinovima Amonovim.
Amma Ishmayel ɗan Netaniya da mutanensa takwas suka tsere daga Yohanan suka gudu zuwa wurin Ammonawa.
16 Tada Johanan, sin Kareahov, i svi vojni zapovjednici koji bijahu s njim uzeše sav preostali narod što ga Jišmael, sin Netanijin, pošto ubi Gedaliju, sina Ahikamova, bijaše doveo iz Mispe: muškarce, žene i djecu i dvorjane koje dovede iz Gibeona.
Sai Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojojin da suke tare da shi suka bi da dukan waɗanda suka tsira daga Mizfa waɗanda ya karɓe daga Ishmayel ɗan Netaniya bayan ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wato, sojoji, mata, yara da fadawan da ya kawo daga Gibeyon
17 Krenuše, a kod Svratišta Kimhama, koje je kraj Betlehema, oni se odmarahu da bi mogli nastaviti put i stići u Egipat,
Sai suka ci gaba, suka dakata a Gerut Kimham kusa da Betlehem a kan hanyarsu zuwa Masar
18 što dalje od Kaldejaca, kojih se bojahu: jer je Jišmael, sin Netanijin, ubio Gedaliju, sina Ahikamova, koga kralj babilonski bijaše postavio za namjesnika u zemlji.
don su kuɓuce wa Babiloniyawa. Sun ji tsoronsu domin Ishmayel ɗan Netaniya ya kashe Gedaliya ɗan Ahikam, wanda sarkin Babilon ya naɗa gwamna a kan ƙasar.

< Jeremija 41 >