< Jeremija 29 >

1 Evo, ovo su riječi poslanice koju prorok Jeremija iz Jeruzalema posla Ostatku izgnanstva - starješinama, svećenicima i prorocima i svemu preostalom narodu što ga Nabukodonozor iz Jeruzalema bijaše odveo u Babilon,
Ga abin da yake cikin wasiƙar annabi Irmiya da ya aika daga Urushalima zuwa ga sauran dattawan da suka ragu a cikin masu zaman bauta da kuma zuwa ga firistoci, annabawa da kuma dukan sauran mutanen da Nebukadnezzar ya kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
2 pošto kralj Jekonija i kraljica-majka, dvorjanici, odličnici judejski i jeruzalemski, kovači i bravari ostaviše Jeruzalem.
(Wannan ya faru bayan Sarki Yekoniya da mahaifiyar sarauniya, shugabannin fada da kuma dukan shugabannin Yahuda da Urushalima, gwanayen sana’a da masu sassaƙa suka tafi zaman bauta daga Urushalima.)
3 Poslanica je poslana po Elasi, sinu Šafanovu, i Gemarji, sinu Hilkijinu, koje Sidkija, kralj judejski, posla u Babilon Nabukodonozoru, kralju babilonskom. Evo sadržaja:
Ya ba da wasiƙar ta hannun Eleyasa ɗan Shafan da Gemariya ɗan Hilkiya, waɗanda Zedekiya sarkin Yahuda ya aika wurin Sarki Nebukadnezzar a Babilon. Wasiƙar ta ce,
4 “Ovako govori Jahve nad Vojskama, kralj Izraelov: 'Svima izgnanicima koje odvedoh iz Jeruzalema u Babilon!
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ga dukan waɗanda aka kwashe zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon.
5 Gradite kuće i nastanite se, sadite vrtove i uživajte urod njihov!
“Ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.
6 Ženite se i rađajte sinove i kćeri! Ženite svoje sinove i udajite svoje kćeri da i oni rađaju sinove i kćeri! Množite se da se ne smanjite!
Ku yi aure ku kuma haifi’ya’ya maza da mata; ku nemi mata wa’ya’yanku maza, ku kuma ba da’ya’yanku mata ga aure, saboda su ma za su haifi’ya’ya maza da mata. Ku riɓaɓɓanya a can, kada ku ragu.
7 Ištite mir zemlji u koju vas izagnah, molite se za nju Jahvi, jer na njezinu miru počiva i vaš mir!'
Haka kuma, ku nemi zaman salama da cin gaba a birnin da aka kai ku zaman bauta. Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda birnin, domin in ya ci gaba, ku ma za ku ci gaba.”
8 Ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov: 'Ne dajte da vas obmanjuju vaši proroci koji su među vama, vaši gataoci! Ne povodite se za snovima koje oni sanjaju!
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa, “Kada ku bar annabawa da masu sihiri a cikinku su ruɗe ku. Kada ku saurari mafarkan da dā kuke ƙarfafa su su yi.
9 Jer oni vam laž prorokuju u moje ime, a ja ih nisam poslao' - riječ je Jahvina.”
Suna muku annabcin ƙarya da sunana. Ban aike su ba,” in ji Ubangiji.
10 Jer ovako govori Jahve: 'Istom kad se Babilonu ispuni onih sedamdeset godina, ja ću vas pohoditi te vam ispuniti dobro obećanje da ću vas vratiti na ovo mjesto.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Sa’ad da shekaru saba’in suka cika a Babilon, zan zo muku in cika alkawarin alherina don in komo da ku zuwa wannan wuri.
11 Jer ja znam svoje naume koje s vama namjeravam - riječ je Jahvina - naume mira, a ne nesreće: da vam dadnem budućnost i nadu.
Gama na san shirye-shiryen da na yi muku,” in ji Ubangiji, “shirye-shiryen cin gaba ba na cutarwa ba, shirye-shiryen ba ku sa zuciya da kuma na nan gaba.
12 Tada ćete me zazivati, dolaziti k meni, moliti mi se i ja ću vas uslišati.
Sa’an nan za ku kira gare ni ku zo ku kuma yi addu’a gare ni, zan kuwa ji ku.
13 Tražit ćete me i naći me jer ćete me tražiti svim srcem svojim.
Za ku neme ni ku kuwa same ni sa’ad da kuka neme ni da dukan zuciyarku.
14 I pustit ću da me nađete - riječ je Jahvina. Izmijenit ću udes vaš i sabrati vas iz svih naroda i sa svih mjesta kamo vas odagnah - riječ je Jahvina. I vratit ću vas na mjesto odakle vas u izagnanstvo odvedoh.
Za ku same ni,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku daga bauta. Zan tattaro ku daga dukan al’ummai in sa ku inda na kore ku,” in ji Ubangiji, “zan kuma komo da ku zuwa wurin da na kwashe ku zuwa zaman bauta.”
15 Istina, vi velite: 'Jahve nam podiže proroke u Babilonu.'
Za ku iya ce, “Ubangiji ya tā da annabawa saboda mu a Babilon.”
16 Ovako govori Jahve kralju koji sjedi na prijestolju Davidovu, i svemu narodu koji živi u ovome gradu - braći vašoj što ne moradoše s vama u izgnanstvo.
Amma ga abin da Ubangiji yana cewa game da sarki, wanda yake zaune a kursiyin Dawuda da kuma dukan mutanen da suka ragu a wannan birni,’yan’uwanku waɗanda ba su tafi tare da ku zuwa zaman bauta ba.
17 Ovako govori Jahve nad Vojskama: “Evo šaljem na njih mač, glad i kugu; učinit ću da budu kao pokvarene smokve, tako loše da nisu za jelo.
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Zan aika da takobi, yunwa da annoba a kansu zan kuma sa su zama kamar ɓaure marar amfani da suka yi munin da ba a iya ci.
18 I gonit ću ih mačem, glađu i kugom i učinit ću ih užasom svim kraljevstvima zemaljskim, prokletstvom, strahotom, ruglom i sramotom svim narodima kamo ih otjeram.
Zan fafare su da takobi, yunwa da annoba zan kuma sa su zama abin ƙyama ga dukan mulkokin duniya da kuma abin la’ana da abin bantsoro, abin dariya da abin reni, a cikin dukan al’umman da aka kore su zuwa.
19 Jer ne poslušaše riječi mojih - riječ je Jahvina - premda sam im svejednako slao sluge svoje proroke, ali ih oni ne poslušaše - riječ je Jahvina.
Gama ba su saurari maganata ba,” in ji Ubangiji, “maganar da na aika gare su sau da sau ta bayina annabawa. Ku kuma masu zaman bauta ba ku saurara ba,” in ji Ubangiji.
20 Ali vi, izgnanici, koje poslah iz Jeruzalema u Babilon, poslušajte svi riječ Jahvinu!”
Saboda haka, ku ji maganar Ubangiji, dukanku masu zaman bauta waɗanda na aika daga Urushalima zuwa Babilon.
21 Ovako govori Jahve nad Vojskama, kralj Izraelov, o Ahabu, sinu Kolajinu, i o Sidkiji, sinu Maasejinu, koji vam laž prorokuje u moje ime: “Evo, predajem ih u ruke Nabukodonozora, kralja babilonskoga, da ih pogubi vama na oči.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa game da Ahab ɗan Kolahiya da Zedekiya ɗan Ma’asehiya, waɗanda suke muku annabcin ƙarya da sunana. “Zan ba da su ga Nebukadnezzar sarkin Babilon, zai kuwa kashe su a gaban idanunku.
22 I njima će se kao kletvom proklinjati svi izgnanici koji su u Babilonu: 'Neka Jahve učini s tobom kao sa Sidkijom i Ahabom koje kralj babilonski ispeče na vatri
Saboda su, dukan masu zaman bauta daga Yahuda waɗanda suke a Babilon za su yi amfani da wannan la’ana cewa, ‘Ubangiji ka yi da mu kamar Zedekiya da Ahab waɗanda sarkin Babilon ya ƙone da wuta.’
23 jer u Izraelu počiniše sramotu čineći preljub sa ženama svojih bližnjih i govoreći u moje ime lažne riječi koje im ja nisam zapovjedio. Ja to znam, i svjedok sam tome' - riječ je Jahvina!”
Gama sun aikata munanan abubuwa a Isra’ila; sun yi zina da matan maƙwabtansu kuma da sunana suka yi ƙarya, waɗanda ban faɗa musu su yi ba. Na san wannan kuma ni shaida ne ga haka,” in ji Ubangiji.
24 A Šemaji ćeš Nehelamcu poručiti:
Faɗa wa Shemahiya mutumin Nehelam,
25 “Ovako govori Jahve nad Vojskama, Bog Izraelov: Ti si u svoje ime poslao pisma svemu narodu koji je u Jeruzalemu, i svećeniku Sefaniji, sinu Maasejinu, i svim ostalim svećenicima:
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka aika da wasiƙu da sunanka ga dukan mutane a Urushalima, zuwa ga Zefaniya ɗan Ma’asehiya firist da kuma ga sauran firistoci. Ka ce wa Zefaniya,
26 'Jahve te postavi svećenikom namjesto svećenika Jojade da paziš u Domu Jahvinu na svakog luđaka koji se gradi prorokom i da ga baciš u klade, sa željezom oko vrata.
‘Ubangiji ya naɗa ka firist a wurin Yehohiyada don ka lura da gidan Ubangiji; ya kamata ka sa kowane mahaukaci wanda yake yi kamar annabi cikin turu da kuma a kangi.
27 Zašto, dakle, nisi spriječio Jeremiju iz Anatota, koji se među vama gradi prorokom?
To, me ya sa ba ka tsawata wa Irmiya daga Anatot, wanda yana ɗauka kansa annabi a cikinku ba?
28 TÓa on nam je poslao poruku u Babilon: Dugo će još trajati: Gradite kuće i nastanite se! Sadite vrtove i uživajte urod njihov!'”
Ya aiko mana da saƙonsa a Babilon cewa zai ɗauki lokaci ƙwarai. Saboda haka ku gina gidaje ku zauna; ku dasa gonaki ku kuma ci abin da suka haifar.’”
29 Svećenik Sefanija pročita pismo proroku Jeremiji.
Zefaniya firist kuwa, ya karanta wasiƙar annabi Irmiya.
30 Tada dođe riječ Jahvina Jeremiji:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
31 “Pošalji svim izgnanicima ovu vijest: 'Ovako govori Jahve o Šemaji Nehelamcu: Jer vam Šemaja prorokuje te vam budi varave nade, premda ga ja nisam poslao,
“Ka aika da wannan saƙo zuwa ga dukan masu zaman bauta cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa game da Shemahiya, mutumin Nehelam. Domin Shemahiya ya yi muku annabci, ko da yake ban aike shi ba, ya kuma sa kuka gaskata ƙarya,
32 ovako govori Jahve: Kaznit ću Šemaju Nehelamca, njega i potomstvo njegovo: nitko mu neće preostati usred ovoga naroda da doživi sreću koju spremam narodu svojemu - riječ je Jahvina - jer je propovijedao pobunu protiv Jahve.'”
ga abin da Ubangiji yana cewa, tabbatacce zan hukunta Shemahiya mutumin Nehelam da zuriyarsa. Ba zai kasance da wani da ya rage a cikin wannan mutane ba, ba kuwa zai ga abubuwa alherin da zan yi wa mutanena ba, in ji Ubangiji, domin ya yi wa’azin tawaye a kaina.’”

< Jeremija 29 >