< Postanak 43 >

1 Strašna glad pritisla zemlju.
A yanzu, yunwa ta yi tsanani a ƙasar.
2 Kad su pojeli hranu koju bijahu donijeli iz Egipta, njihov im otac reče: “Idite opet i nabavite nam malo hrane.”
Saboda haka sa’ad da suka cinye dukan hatsin da suka kawo daga Masar, mahaifinsu ya ce musu, “Ku koma, ku sayo mana ƙarin abinci.”
3 Nato će mu Juda: “Onaj nam je čovjek jasno rekao: 'Ne smijete preda me ako vaš brat ne bude s vama.'
Amma Yahuda ya ce masa, “Mutumin ya gargaɗe mu sosai cewa, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai in ɗan’uwanku yana tare da ku.’
4 Ako si, dakle, voljan s nama poslati našega brata, mi ćemo otići dolje i kupit ćemo ti žita.
In za ka aika da ɗan’uwanmu tare da mu, za mu gangara mu sayo maka abinci.
5 Ali ako njega ne pustiš s nama, onda mi tamo i ne idemo, jer nam je onaj zaprijetio: 'Ne smijete preda me ako vaš brat ne bude s vama.'”
Amma in ba za ka aika da shi ba, ba za mu gangara ba, gama mutumin ya ce mana, ‘Ba za ku sāke ganin fuskata ba sai ko in ɗan’uwanku yana tare da ku.’”
6 “Zašto ste mi”, zapita Izrael, “nanijeli jad rekavši onom čovjeku da imate još jednoga brata?”
Isra’ila ya yi tambaya, “Me ya sa kuka kawo wannan damuwa a kaina ta wurin faɗa wa mutumin cewa kuna da wani ɗan’uwa?”
7 Oni odgovore: “Čovjek nas je neprestano zapitkivao o nama i o našoj obitelji: 'Je li vam još živ otac? Imate li još kojega brata?' Mi smo mu odgovarali na pitanja. Kako smo mogli znati da će reći: 'Dovedite svoga brata!'”
Suka amsa, “Mutumin ya yi mana tambaya sosai game da kanmu da iyalinmu. Ya tambaye mu, ‘Mahaifinku yana da rai har yanzu? Kuna da wani ɗan’uwa?’ Mu dai mun amsa tambayoyinsa ne. Ta yaya za mu sani zai ce, ‘Ku kawo ɗan’uwanku a nan’?”
8 Potom Juda reče svome ocu Izraelu: “Pusti dječaka sa mnom pa da se dignemo i krenemo; tako ćemo preživjeti, a ne pomrijeti, i mi, i ti, i naša djeca.
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Isra’ila mahaifinsa, “Ka aika saurayin tare da ni za mu kuwa tafi nan da nan, saboda mu da’ya’yanmu mu rayu, kada mu mutu.
9 Ja za nj jamčim; mene drži odgovornim za nj. Ako ga tebi ne vratim i preda te ga ne dovedem, bit ću ti kriv svega vijeka.
Ni kaina zan tabbatar da lafiyarsa; na ɗauki lamuninsa, a hannuna za ka neme shi. In ban dawo da shi gare ka, in sa shi nan a gabanka ba, zan ɗauki laifin a gabanka dukan kwanakina.
10 TÓa da nismo toliko oklijevali, mogli smo se već i dvaput vratiti.”
Ai, da ba mun jinkirta ba, da mun komo har sau biyu.”
11 Njihov otac Izrael reče im: “Kad je tako, neka bude, ali učinite ovo: metnite u torbe najbiranijih proizvoda ove zemlje i ponesite na dar onom čovjeku: nešto balzama, nešto meda i mirodija, mirisne smole, pa lješnjaka i badema.
Sa’an nan mahaifinsu Isra’ila ya ce musu, “In dole ne a yi haka, to, sai ku yi. Ku sa waɗansu amfani mafi kyau na ƙasar a buhunanku, ku ɗauka zuwa wurin mutumin a matsayin kyauta, da ɗan man ƙanshi na shafawa, da kuma’yar zuma, da kayan yaji, da ƙaro, da tsabar citta da kuma almon.
12 Sa sobom uzmite dvostruko novaca, jer treba vratiti novac koji ste našli u grlima svojih vreća. Možda je ono bila zabuna.
Ku ɗauki ninki biyu na yawan azurfa tare da ku, gama dole ku mayar da azurfan da aka sa a cikin bakunan buhunanku. Mai yiwuwa an yi haka a kuskure ne.
13 Uzmite svoga brata pa se opet zaputite onom čovjeku.
Ku ɗauki ɗan’uwanku kuma ku koma wurin mutumin nan da nan.
14 Neka Bog Svemogući, El Šadaj, potakne onog čovjeka na milosrđe prema nama te vam pusti i drugoga brata i Benjamina. A ja, moram li bez djece ostati, neka ostanem.”
Bari Allah Maɗaukaki yă nuna muku alheri a gaban mutumin saboda yă bar ɗan’uwanku da Benyamin su dawo tare da ku. Ni kuwa, in na yi rashi, na yi rashi.”
15 Uzmu ljudi darove; uzmu sa sobom dvostruko novaca, povedu Benjamina te siđu u Egipat i stupe pred Josipa.
Saboda haka mutanen suka ɗauki kyautar, da kuma kuɗin da ya ninka na farko. Suka kuma ɗauki Benyamin, suka gaggauta suka gangara zuwa Masar suka kuma gabatar da kansu ga Yusuf.
16 Kad Josip ugleda s njima Benjamina, reče upravitelju svoga kućanstva: “Odvedi ljude u kuću, zakolji jedno živinče i pripremi, jer će ovi ljudi blagovati sa mnom o podne!”
Sa’ad da Yusuf ya ga Benyamin tare da su, sai ya ce wa mai hidimar gidansa, “Ka shigar da mutanen cikin gida, ka yanka dabba ka shirya, gama mutanen za su ci abincin rana tare da ni.”
17 Čovjek učini kako je Josip rekao i povede ljude u Josipov dom.
Mutumin ya yi kamar yadda Yusuf ya faɗa masa, ya kuwa ɗauki mutanen zuwa gidan Yusuf.
18 Ljudi se pobojaše kad su bili povedeni u dom Josipov te rekoše: “Zbog novca koji se našao u našim vrećama prvi put vode nas unutra tako da nas napadnu i zajedno s našom magaradi uzmu za robove.”
Mutanen dai suka firgita sa’ad da aka ɗauke su zuwa gidansa. Suka yi tunani, “An kawo mu nan ne saboda azurfan da aka sa a cikin buhunanmu da farko. Yana so yă fāɗa mana, yă kuma sha ƙarfinmu, yă ƙwace mu kamar bayi, yă kuma kwashe jakunanmu.”
19 Stoga se primaknu upravitelju Josipova doma te mu, na ulazu u kuću, reknu:
Saboda haka suka je wurin mai yin wa Yusuf hidima, suka yi masa magana a bakin ƙofar gida.
20 “Oprosti, gospodaru! Mi smo i prije jednom dolazili da nabavimo hrane;
Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun zo nan ƙaro na farko don mu saya abinci,
21 i kad smo stigli na prenoćište i otvorili svoje vreće, a to novac svakoga od nas ozgo u njegovoj vreći, naš novac, ista svota. Sad smo ga donijeli sa sobom.
amma a inda muka tsaya don mu kwana, da muka buɗe buhunanmu sai kowannenmu ya sami azurfansa daidai a bakin buhunsa. Saboda haka ga kuɗin a hannunmu, mun sāke komowa da su.
22 A ponijeli smo i drugog novca da kupimo hrane. Mi ne znamo tko nam je stavio novac u naše vreće.”
Mun kuma kawo ƙarin azurfa tare da mu don mu saya abinci. Ba mu san wa ya sa azurfanmu a cikin buhunanmu ba.”
23 “Budite mirni”, reče im on. “Ne bojte se! Bog vaš i Bog vašega oca stavio je blago u vaše vreće. Vaš je novac k meni stigao.” Potom im izvede Šimuna.
Sai mai hidimar ya ce, “Ba kome, kada ku ji tsoro. Allahnku, Allahn mahaifinku ne ya ba ku dukiyar a cikin buhunanku; ni dai, na karɓi azurfanku.” Sa’an nan ya fitar musu da Simeyon.
24 Čovjek zatim uvede ljude u Josipovu kuću; dade im vode da operu noge, a njihovoj magaradi baci p§iće.
Mai yin hidimar ya ɗauki mutane zuwa gidan Yusuf ya ba su ruwa su wanke ƙafafunsu, ya kuma tanada wa jakunansu abinci.
25 Potom priprave oni svoje darove za dolazak Josipov o podne, jer su čuli da će ondje ručati.
Suka shirya kyautansu domin isowar Yusuf da rana, gama sun ji cewa zai ci abinci a nan.
26 Kad je Josip došao u kuću, dadu mu darove koje su sa sobom donijeli i do zemlje mu se poklone.
Sa’ad da Yusuf ya zo gida, sai suka ba shi kyautai da suka kawo, suka rusuna a gabansa har ƙasa.
27 Upita ih on za zdravlje te će dalje: “A je li dobro vaš stari otac o kome ste mi govorili? Je li još dobra zdravlja?”
Ya tambaye su, yaya suke, sa’an nan ya ce, “Yaya tsohon nan mahaifinku da kuka faɗa mini? Yana da rai har yanzu?”
28 “Sluga tvoj, otac naš, dobro je i još je dobra zdravlja”, odgovore i duboko se naklone iskazujući poštovanje.
Suka amsa, “Bawanka mahaifinmu yana da rai har yanzu da kuma ƙoshin lafiya.” Suka kuma rusuna suka yi mubaya’a.
29 Podigavši svoje oči, Josip opazi svoga brata Benjamina - sina svoje majke - te upita: “Je li ovo vaš najmlađi brat o kome ste mi govorili?” Onda nastavi: “Bog ti bio milostiv, sine moj!”
Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
30 Josip se poslije toga požuri van jer mu se srce uzbudilo zbog brata; bilo mu je da zaplače. Uđe u jednu sobu i tu se isplaka.
Saboda motsi mai zurfi da zuciyarsa ta yi da ganin ɗan’uwansa, sai Yusuf ya gaggauta ya fita, ya nemi wuri yă yi kuka. Ya shiga ɗakinsa ya yi kuka a can.
31 Onda opere lice, ponovo se javi i, svladavajući se, naredi: “Poslužite ručak!”
Bayan ya wanke fuskarsa, sai ya fito ya daure, ya umarta, “A kawo abinci.”
32 Staviše njemu napose, njima napose, a napose opet Egipćanima koji su s njim jeli. Egipćani ne bi mogli jesti s Hebrejima, jer bi to Egipćanima bilo odvratno.
Sai aka raba musu abinci, nasa shi kaɗai su kuma su kaɗai, domin Masarawa ba sa cin abinci tare da Ibraniyawa, gama wannan abin ƙyama ne ga Masarawa.
33 I kad posjedaše pred njim, najstariji prema starosti svojoj, a najmlađi prema mladosti svojoj, samo se zgledahu.
Aka zaunar da’yan’uwan Yusuf a gabansa bisa ga shekarunsu, daga ɗan fari zuwa auta.’Yan’uwan kuwa suka duddubi juna suna mamaki.
34 I naređivaše on da jela ispred njega nose njima, a obrok Benjaminov bijaše pet puta veći od svih ostalih. I pili su i gostili se s njim.
Daga teburin da yake a gaban Yusuf aka riƙa ɗibar rabonsu ana kai musu, amma rabon Benyamin ya yi biyar ɗin na kowannensu. Suka kuwa sha, suka yi murna tare da shi.

< Postanak 43 >