< Ezra 4 >

1 Ali kada su čuli Judini i Benjaminovi neprijatelji da povratnici iz sužanjstva grade svetište Jahvi, Bogu Izraelovu,
Sa’ad da abokan gāban Yahuda da na Benyamin suka ji cewa waɗanda suka dawo daga bauta suna gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila
2 potražiše Zerubabela, Ješuu i glavare obiteljske i rekoše im: “Mi želimo s vama graditi, jer, kao i vi, tražimo Boga vašega i njemu prinosimo žrtve od vremena Esar Hadona, asirskoga kralja, koji nas je ovamo doveo.”
sai suka zo wurin Zerubbabel da kuma wurin shugabannin iyalai, suka ce, “Bari mu taimake ku ginin domin mu ma muna addu’a ga Allahnku yadda kuke yi, muna miƙa masa hadaya tun lokacin Esar-Haddon sarkin Assuriya wanda ya kawo mu nan.”
3 Zerubabel, Ješua i glavari izraelskih obitelji odgovoriše im: “Nije na vama da s nama gradite Dom našemu Bogu: gradit ćemo mi sami Jahvi, Bogu Izraelovu, kako nam je naredio Kir, kralj perzijski.”
Amma Zerubbabel, Yeshuwa, da sauran shugabannin iyalai na Isra’ila suka amsa suka ce, “Ba za ku sa hannu cikin gina wa Allahnmu haikali ba, mu kaɗai za mu gina wa Ubangiji, Allah na Isra’ila gini kamar yadda Sarki Sairus, sarkin Farisa, ya umarce mu.”
4 Tada je narod one zemlje plašio ljude Judeje i smetao im u gradnji.
Sai mutanen da suke zama a wurin suka fara yin ƙoƙari su sa mutanen Yahuda su karaya, suka sa su ji tsoron ci gaba da ginin.
5 Podmitili su savjetnike da im ometaju naum: tako je bilo za vrijeme perzijskoga kralja Kira sve do perzijskoga kralja Darija. Samarijanske smetnje za Kserksove i Artakserksove vladavine
Suka yi hayar mashawarta don su ga cewa sun ɓata ƙoƙarinsu dukan kwanakin mulkin Sairus sarkin Farisa har zuwa kwanakin mulkin Dariyus sarkin Farisa.
6 Za Kserksova kraljevanja, na početku njegove vladavine, sastaviše tužbu protiv stanovnika Judeje i Jeruzalema.
A farkon mulkin Zerzes, sai abokan gāba suka kawo ƙarar mutanen Yahuda da na Urushalima.
7 I za vremena Artakserksova pisali su Bišlam, Mitredat, Tabel i ostali njihovi drugovi protiv Jeruzalema perzijskom kralju Artakserksu. Podnesak je bio pisan aramejskim pismom i jezikom.
A zamanin Artazerzes sarkin Farisa kuma, sai Bishlam, da Mitredat, da Tabeyel, da sauran abokansu suka rubuta wasiƙa zuwa ga Artazerzes. Aka rubuta wasiƙar da harufan Arameyik, aka kuma fassara ta a yaren Arameyik.
8 Zatim su upravitelj Rehum i tajnik Šimšaj napisali kralju Artakserksu slijedeće pismo protiv Jeruzalema -
Rehum shugaban rundunar soja, da Shimshai marubuci, suka rubuta wasiƙar a kan Urushalima zuwa ga sarki Artazerzes, suka ce.
9 upravitelj Rehum, tajnik Šimšaj i ostali drugovi njihovi: perzijski suci, poslanici, činovnici; Arkevajci, Babilonci, Suzanci - to jest Elamci -
Rehum shugaban sojoji, da Shimshai marubuci, da sauran abokansu, wato, alƙalai, da masu riƙe da muƙamai daga Farisa, Uruk da Babilon, mutanen Elam da na Shusha,
10 i ostali narodi koje je veliki i slavni Asurbanipal bio odveo u sužanjstvo i naselio ih u gradove Samarije i druge krajeve s onu stranu Rijeke.
da sauran mutane waɗanda mai girma Osnaffar ya kwaso, ya zaunar da su cikin birnin Samariya da sauran wurare na Kewayen Kogin Yuferites.
11 Evo prijepisa pisma koje su mu poslali: “Kralju Artakserksu, tvoje sluge, ljudi s onu stranu Rijeke. Sada, dakle,
(Ga abin da suka rubuta.) Zuwa ga sarki Artazerzes. Daga bayinka, mutanen Kewayen Kogin Yuferites.
12 neka zna kralj da su Judejci stigli k nama od tebe; došavši u Jeruzalem, žele ponovo sagraditi odmetnički i opaki grad; podižu zidine, a temelje su već postavili.
Ya kamata sarki ya san cewa Yahudawan da suka hauro wurinmu daga wurinka, sun je Urushalima suna sāke gina wannan mugun birni mai tawaye. Suna sāke gyara katangar, suna kuma gyara harsashin katangar.
13 Neka zna kralj: ako ovaj grad bude sagrađen i zidovi podignuti, neće se više plaćati porez, ni danak, ni carina, i ovaj će grad biti na štetu kraljevske riznice.
Ya kamata fa, sarki ya san cewa in aka sāke gina wannan birni duk da katangar birnin, mutanen birnin ba za su dinga biyan haraji, da kuɗin shiga, da na fitar da kaya ba, wannan zai sa aljihun masarauta yă bushe.
14 Budući da jedemo dvorsku sol, ne čini nam se doličnim gledati ovu sramotu nanesenu kralju. Zato, dakle, obavještavamo kralja:
Tun da yake muna ƙarƙashin fada, bai kyautu mu bari a rena sarki ba, Saboda haka muke sanar da sarki,
15 neka se poduzmu istraživanja u ljetopisima tvojih očeva: u tim ćeš ljetopisima naći i utvrditi da je ovaj grad odmetnički grad, nesretan za kraljeve i pokrajine i da su se u njemu od davnine dizale bune. Zato je ovaj grad bio razoren.
domin a bincika a littattafan tarihin kakanninka. Za ka ga cewa wannan birni mai tawaye ne. Tun daga zamanin dā wannan birnin yana ba sarakuna da yankuna damuwa. Wannan ne ya sa aka ragargazar da birnin.
16 Obavješćujemo kralja da neće biti više tvoje područje preko Rijeke ako ovaj grad bude ponovo sagrađen i zidovi podignuti!”
Muna sanar da sarki cewa in har aka sāke gina wannan birnin da katangarsa, zai zama ka rasa kome a gefen Kewayen Kogin Yuferites ke nan.
17 Kralj je poslao ovaj odgovor: “Rehumu, upravitelju, Šimšaju, tajniku, i ostalim drugovima njihovim koji borave u Samariji i drugdje, s onu stranu Rijeke - mir! Evo,
Sarki ya aika da wannan amsa. Zuwa ga Rehum shugaban sojoji, Shimshai marubuci da kuma sauran abokansu waɗanda suke zama a Samariya da kuma sauran wurare a Kewayen Kogin Yuferites. Gaisuwa.
18 podnesak koji ste mi poslali bio je preda mnom pričitan u njegovu prijevodu.
An karanta, an kuma fassara mini wasiƙar da kuma aika.
19 Po mojoj su naredbi poduzeli istraživanja i utvrdili da se taj grad dizao od davnine protiv kraljeva i da su u njemu bivali ustanci i bune.
Na ba da umarni aka kuma yi bincike, aka tarar cewa wannan birni ya daɗe yana yi wa sarakuna tawaye, an yi tashin hankali a birnin.
20 I moćni su kraljevi kraljevali u Jeruzalemu, koji su gospodarili svime s onu stranu Rijeke: njima se plaćao danak, porez i carina.
Urushalima ta yi sarakuna masu iko sosai waɗanda suka yi mulkin Kewayen Kogin Yuferites gaba ɗaya, an kuma biya masu haraji, da kuɗin shiga da na fita na kaya.
21 Zapovjedite, dakle, da se prekine pothvat onih ljudi: taj se grad neće zidati dok ja o tome ne odlučim.
Saboda haka sai ku ba da umarni yanzu cewa mutanen su daina wannan aiki sai lokacin da na ba da umarni.
22 Čuvajte se svakog propusta u postupku, da ne bi zlo poraslo na štetu kraljeva.”
Ku tabbata ka ɗauki wannan da muhimmanci. Don me za a bari wannan abu yă zama abin damuwa ga sarauta?
23 Pošto je prijepis otpisa kralja Artakserksa pročitan pred Rehumom, upraviteljem, Šimšajem, tajnikom, i pred njihovim drugovima, oni brzo odoše u Jeruzalem k Judejcima te im oružanom snagom zabraniše radove.
Da gama karanta wasiƙar sarki Artazerzes wa Rehum da Shimshai marubuci, da abokansu, sai suka yi sauri suka je wurin Yahudawa a Urushalima, suka hana su aikin ƙarfi da yaji.
24 Tako su obustavljeni poslovi oko gradnje Doma Božjega u Jeruzalemu. Bili su prekinuti sve do druge godine kraljevanja Darija, perzijskoga kralja.
Saboda haka aikin a gidan Allah a Urushalima ya tsaya cik sai a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus sarkin Farisa.

< Ezra 4 >