< Izlazak 7 >
1 Mojsiju je Jahve odgovorio: “Vidi! Faraonu ću te nametnuti kao božanstvo; tvoj brat Aron bit će tvoj prorok.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Duba, na maishe ka kamar Allah ga Fir’auna, ɗan’uwanka Haruna kuma zai zama annabinka.
2 Ti kazuj sve što ti naređujem, a tvoj brat Aron neka faraonu ponovi da pusti Izraelce te odu iz njegove zemlje.
Za ka faɗi kome da na umarce ka, ɗan’uwanka Haruna kuwa zai faɗa wa Fir’auna, yă bar Isra’ilawa su fita daga ƙasarsa.
3 Ja ću učiniti da otvrdne srce faraonu i umnožit ću znakove i čudesa u zemlji egipatskoj.
Amma zan taurare zuciyar Fir’auna, kuma ko da na ninka mu’ujizai da kuma alamu a Masar,
4 Kako vas faraon neće poslušati, ja ću staviti svoju ruku na Egipat: strašno kažnjavajući, izbavit ću svoje čete, narod svoj, Izraelce, iz egipatske zemlje.
ba zai saurare ku ba. Don haka zan miƙa hannuna a kan Masar, in murƙushe ta da bala’i iri-iri, bayan haka zan fitar da taron mutanen Isra’ila daga ƙasar Masar ta wurin hukuntaina masu girma.
5 Kad pružim svoju ruku na Egipat i izvedem Izraelce iz njihove sredine, tada će Egipćani spoznati da sam ja Jahve.”
Masarawa kuwa za su san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na miƙa hannuna a kan Masar, na kuma fitar da Isra’ilawa daga gare ta.”
6 Mojsije i Aron poslušaše: kako im je Jahve naredio, upravo tako učiniše.
Musa da Haruna suka aikata yadda Ubangiji ya umarce su.
7 Mojsiju je bilo osamdeset, a Aronu osamdeset i tri godine kad su faraonu postavili svoje zahtjeve.
Musa yana da shekara tamanin da haihuwa, Haruna kuma yana da shekara tamanin da uku, sa’ad da suka yi magana da Fir’auna.
8 Još doda Jahve Mojsiju i Aronu:
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
9 “Kad faraon zatraži od vas da izvedete kakvo znamenje, ti reci Aronu da uzme svoj štap i baci ga pred faraona, a štap će se pretvoriti u zmiju.”
“Sa’ad da Fir’auna ya ce muku, ‘Aikata wani al’ajabi,’ sai ka ce wa Haruna, ‘Ɗauki sandanka ka jefa shi a ƙasa, a gaban Fir’auna,’ zai kuwa zama maciji.”
10 Dođu Mojsije i Aron pred faraona i učine kako im je Jahve naredio. Aron baci pred faraona i njegove službenike svoj štap, koji se pretvori u zmiju.
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna, suka yi yadda Ubangiji ya umarce su. Haruna ya jefa sandansa ƙasa, a gaban Fir’auna da bayinsa, sai sandan ya zama maciji.
11 Zovne faraon mudrace i vračare. I zaista, egipatski vračari svojim vračanjem učine isto:
Fir’auna kuwa ya kira masu hikima da masu sihiri, sai bokayen Masarawa ma suka yi irin abubuwan nan da bokancinsu.
12 svaki baci svoj štap, koji se pretvori u zmiju. Ali Aronov štap proguta njihove štapove.
Kowannensu ya jefa sandansa ƙasa, ya kuwa zama maciji. Amma sandan Haruna ya haɗiye sandunansu.
13 Faraon bijaše tvrdokorna srca: ne htjede poslušati Mojsija i Arona, kako je Jahve i kazao.
Duk da haka zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurare su ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
14 Tada Jahve reče Mojsiju: “Faraonovo je srce okorjelo; odbija da pusti narod.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Zuciyar Fir’auna taurariya ce, ya ƙi yă bar mutanen su tafi.
15 Ujutro pođi k faraonu. Kad izađe k vodi, stani preda nj na obali Rijeke. Uzmi u ruku štap što se bio u zmiju pretvorio.
Ka je wurin Fir’auna da safe, yayinda za shi kogi. Ka jira a bakin Nilu don ka sadu da shi, ka ɗauki sandan nan da ya canja zuwa maciji a hannunka.
16 Reci mu: 'Jahve, Bog Hebreja, poslao me k tebi s porukom da pustiš moj narod da mi iskaže štovanje u pustinji. Ali sve dosad ti nisi poslušao.
Sa’an nan ka ce masa, ‘Ubangiji, Allah na Ibraniyawa, ya aiko ni in faɗa maka, Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada a hamada. Amma har yanzu ba ka yi biyayya ba.
17 Ovako Jahve poručuje: Ovim ćeš spoznati da sam ja Jahve. Gledaj! Štapom koji imam u ruci mlatnut ću po vodi u Rijeci i pretvorit će se u krv.
Ga abin da Ubangiji ya ce, da wannan za ka san cewa ni ne Ubangiji. Da sandan da yake hannuna zan bugi ruwan Nilu, zai kuma zama jini.
18 Ribe će u Rijeci pocrkati; Rijeka će se usmrdjeti, i grstit će se Egipćanima piti vodu iz Rijeke.'”
Kifi a ciki Nilu za su mutu, ruwan kuma zai yi ɗoyi; Masarawa ba za su iya shan ruwansa ba.’”
19 Još Jahve reče Mojsiju: “Reci Aronu da uzme svoj štap i pruži svoju ruku povrh egipatskih voda: njihovih rijeka, njihovih prokopa, njihovih jezeraca, svih njihovih vodenih stjecišta, da se pretvore u krv; po svoj zemlji egipatskoj neka je krv, čak i u drvenim i kamenim posudama.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka ɗauki sandanka, ka miƙa hannunka kan ruwan Masar, kan kogunansu da rafuffukansu da kududdufansu da kuma dukan tafkunansu, za su zama jini.’ Jini zai kasance ko’ina a Masar, har ma a cikin abubuwan ajiyar ruwansu da aka yi da itace da kuma dutse.”
20 Mojsije i Aron učiniše kako im je Jahve naredio. Podiže Aron svoj štap i naočigled faraona i njegovih službenika mlatnu po vodi u Rijeci. Sva se voda u Rijeci prometnu u krv.
Musa da Haruna suka yi yadda Ubangiji ya umarta. Ya ɗaga sandansa a gaban Fir’auna da bayinsa, ya bugi ruwan Nilu, dukan ruwan kuwa ya zama jini.
21 Ribe u Rijeci pocrkaše; Rijeka se usmrdje, tako da Egipćani nisu mogli piti vodu iz Rijeke; krv bijaše po svoj zemlji egipatskoj.
Kifin da suke cikin Nilu suka mutu, kogin kuwa ya yi wari sosai yadda Masarawa ba su iya shan ruwan ba. Jini ya bazu ko’ina a Masar.
22 Ali egipatski vračari svojim vračanjem učiniše isto. Tako faraon ostade tvrdokorna srca: nije htio poslušati Mojsija i Arona, kako je Jahve i kazao.
Amma bokayen Masar ma suka yi abubuwan nan da sihirinsu, sai zuciyar Fir’auna ta taurare; bai saurari Musa da Haruna ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
23 Faraon se okrenu i ode u svoj dvor, ne uzimajući ni to k srcu.
A maimakon yă saurara, sai ya juya ya koma fadarsa, bai ma damu da abin da aka yi ba.
24 Svi su Egipćani počeli kopati oko Rijeke tražeći pitke vode jer nisu mogli piti vode iz Rijeke.
Sai dukan Masarawa suka yi ta tonon gefen Nilu don su sami ruwan sha, domin ba su iya shan ruwan kogin ba.
25 Kad je prošlo sedam dana kako je Jahve udario po Rijeci,
Kwana bakwai suka wuce bayan da Ubangiji ya bugi kogin.