< Izlazak 24 >

1 Potom reče Mojsiju: “Uzađi k Jahvi - ti, Aron, Nadab i Abihu i sedamdeset izraelskih starješina. Poklonite se izdaljega!
Ana nan sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ku hauro zuwa wurina, kai da Haruna, Nadab da Abihu, da kuma dattawa saba’in a cikin Isra’ila. Za ku yi sujada da ɗan nisa,
2 Neka se sam Mojsije primakne k Jahvi! Oni neka se ne primiču, a puk neka se s njim ne penje.”
sai Musa kaɗai zai kusaci Ubangiji. Amma sauran kada su zo kusa, kada kuma jama’a su hau tare da shi.”
3 Dođe Mojsije i kaza narodu sve riječi Jahvine i sve odredbe. A sav puk odgovori u jedan glas: “Sve riječi što ih Jahve reče, vršit ćemo.”
Sa’ad da Musa ya tafi ya faɗa wa mutanen duk kalmomin Ubangiji da dokokinsa, sai suka amsa da murya ɗaya suna cewa, “Duk abin da Ubangiji ya faɗa, za mu yi.”
4 Tada Mojsije popiše sve riječi Jahvine. A ujutro podrani te podigne žrtvenik na podnožju brda i dvanaest stupova za dvanaest plemena Izraelovih.
Sai Musa ya rubuta duk abin da Ubangiji ya faɗa. Ya tashi kashegari da sassafe ya gina bagade kusa da dutsen, ya aza al’amudai goma sha biyu bisa ga kabilu goma sha biyu na Isra’ila.
5 Zatim naloži mladim Izraelcima da prinesu žrtve paljenice i da žrtvuju Jahvi junce kao žrtve pričesnice.
Sai ya aiki samarin Isra’ilawa, suka miƙa hadaya ta ƙonawa, suka kuma miƙa ƙananan bijimai don hadaya ta salama ga Ubangiji.
6 Mojsije uhvati krv; polovinu krvi ulije u posude, a polovinu izlije po žrtveniku.
Musa ya ɗauki rabin jinin ya zuba a cikin kwanoni, rabin kuma ya yayyafa a kan bagaden.
7 Prihvati zatim Knjigu Saveza pa je narodu glasno pročita, a narod uzvrati: “Sve što je Jahve rekao, izvršit ćemo i poslušat ćemo.”
Sa’an nan ya ɗauki Littafin Alkawari ya karanta wa mutane. Suka amsa suka ce, “Za mu yi duk abin da Ubangiji ya faɗa; za mu yi biyayya.”
8 Mojsije potom uzme krvi te poškropi narod govoreći: “Ovo je krv Saveza koji je Jahve s vama uspostavio na temelju svih ovih riječi.”
Musa ya kuma ɗauki jinin, ya yayyafa a kan mutanen ya ce, “Wannan shi ne jinin alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, bisa ga dukan waɗannan kalmomi.”
9 Onda se uspne Mojsije s Aronom, Nadabom i Abihuom i sa sedamdeset starješina Izraelovih.
Musa da Haruna, Nadab da Abihu, da dattawa saba’in, Allah na Isra’ila suka haura
10 Oni vidješe Boga Izraelova: podnožje njegovim nogama kao da je bilo od dragoga kamena safira, sjajem nalik na samo nebo.
suka kuma ga Allah na Isra’ila. A ƙarƙashin ƙafafunsa akwai wani abu wanda aka yi da saffaya, mai haske kuma kamar sararin sama kansa.
11 Ni ruke svoje nije pružio na izabranike Izraelaca: slobodno su Boga motrili i jeli i pili.
Amma Allah bai yi wa shugabannin Isra’ila wani abu ba; suka ga Allah, suka ci suka kuma sha.
12 Onda Jahve reče Mojsiju: “Popni se k meni na brdo i pričekaj ondje. Dat ću ti kamene ploče sa zakonom i zapovijedima koje sam za njihovu pouku napisao.”
Ubangiji ya ce wa Musa, “Hauro wurina a kan dutse, ka tsaya a nan, zan ba ka allunan dutsen, da doka da umarnan da na rubuta don koyonsu.”
13 Ustane Mojsije i njegov pomoćnik Jošua te se Mojsije popne na brdo Božje.
Sa’an nan Musa ya fita tare da Yoshuwa mataimakinsa, ya kuwa hau kan dutsen Allah.
14 A starješinama reče: “Čekajte nas ovdje dok se ne vratimo. Eto je s vama Aron i Hur. Tko imadne kakvu razmiricu, neka se obrati na njih.”
Ya ce wa dattawan, “Ku jira mu a nan, sai mun dawo wurinku. Haruna da Hur suna tare da ku, in wani yana da wata damuwa, sai yă je wurinsu.”
15 Zatim Mojsije uzađe na brdo, a onda oblak prekri brdo.
Da Musa ya hau dutsen, sai girgije ya rufe dutsen,
16 Slava se Jahvina nastani na Sinajskom brdu i oblak ga obavijaše šest dana. Sedmoga dana zovne Jahve Mojsija isred oblaka.
sai ɗaukakar Ubangiji ta sauka a kan Dutsen Sinai, kwana shida girgije ya rufe dutsen, a rana ta bakwai, sai Ubangiji ya kira Musa daga cikin girgijen.
17 Slava Jahvina na vrhuncu brda bijaše očima Izraelaca kao vatra koja sažiže. Mojsije zađe u oblak i uspne se na brdo.
Ga Isra’ilawa dai, ɗaukakar Ubangiji ta yi kamar wuta mai ci a kan dutse.
18 Četrdeset dana i četrdeset noći boravio je Mojsije na brdu.
Sa’an nan Musa ya shiga girgijen ya hau kan dutsen. Ya zauna a kan dutsen yini arba’in da dare arba’in.

< Izlazak 24 >