< Ponovljeni zakon 27 >

1 Potom Mojsije i starješine izraelske nalože narodu: “Vršite sve zapovijedi što vam ih danas naređujem.
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 Onog dana kad prijeđete preko Jordana u zemlju što ti je daje Jahve, Bog tvoj, podigni sebi veliko kamenje; krečom ga okreči
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 i na njemu ispiši sve riječi ovoga Zakona u trenutku kad budeš ulazio u zemlju što ti je daje Jahve, Bog tvoj, u zemlju kojom teče med i mlijeko, kako ti je rekao Jahve, Bog otaca tvojih.
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 Kada, dakle, prijeđeš preko Jordana, onda to kamenje, kako ti danas zapovijedam, podigni na brdu Ebalu i okreči ga krečom.
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 Ondje sagradi i žrtvenik Jahvi, Bogu svome - žrtvenik od kamenja na koje nisi spuštao gvožđa.
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 Žrtvenik Jahvi, Bogu svome, sagradi od neklesana kamena. Na njemu prinosi paljenice Jahvi, Bogu svome.
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 Prinosi i pričesnice i ondje ih blaguj, radujući se pred Jahvom, Bogom svojim.
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 Ispiši na tom kamenju sve riječi ovoga Zakona: ureži ih dobro.”
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 Zatim Mojsije i levitski svećenici rekoše svemu Izraelu: “Pozor, Izraele, i slušaj! Danas si postao narodom Jahve, Boga svoga.
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 Zato slušaj glas Jahve, Boga svoga, i vrši zapovijedi njegove i zakone njegove koje ti danas naređujem.”
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 Onoga dana naredi Mojsije narodu:
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 “Kad prijeđete preko Jordana, neka ova plemena: Šimun, Levi, Juda, Jisakar, Josip i Benjamin stanu na brdu Gerizimu da blagoslivljaju narod.
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 A ova neka stanu na brdu Ebalu da proklinju: Ruben, Gad, Ašer, Zebulun, Dan i Naftali.
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 Neka onda Levijevci preuzmu riječ i jakim glasom reknu svim Izraelcima:
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 'Proklet bio tko načini kumira, klesana ili livena - zazor Jahvi, djelo rukotvorca, sve ako ga stavi i na potajno mjesto.' - I sav narod neka odgovori: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 'Proklet bio koji vrijeđa oca svoga i majku svoju!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 'Proklet bio koji pomakne međaš susjedov!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 'Proklet bio koji slijepca zavede na stranputicu!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 'Proklet bio koji krnji prava došljaka, sirote i udovice!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 'Proklet bio koji legne sa ženom oca svoga, jer je razgrnuo pokrivač oca svoga!'- I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 'Proklet bio koji legne s bilo kakvom životinjom!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 'Proklet bio koji legne sa svojom sestrom, bila ona kći njegova oca ili kći njegove majke.' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 'Proklet bio koji legne s punicom svojom!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 'Proklet bio koji ubije bližnjega svoga iz potaje!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 'Proklet bio koji primi mito da smrt donese nevinome!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 'Proklet bio koji ne bude držao riječi ovoga Zakona i vršio ih!' - I sav narod neka reče: 'Amen!'
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”

< Ponovljeni zakon 27 >