< 2 Samuelova 20 >
1 Ondje se slučajno našao opak čovjek po imenu Šeba, Bikrijev sin, Benjaminovac. On zatrubi u rog i viknu: “Mi nemamo udjela na Davidu ni baštine na Jišajevu sinu! Svaki svome šatoru, Izraele!”
Akwai wani mai tā-da-na-zaune-tsaye, sunansa Sheba, ɗan Bikri, daga kabilar Benyamin, a wurin. Sai ya busa ƙaho, ya yi ihu ya ce, “Ba mu da rabo a wurin Dawuda, ba mu da sashe a wurin ɗan Yesse! Kowa yă nufi tentinsa, ya Isra’ila!”
2 Tako svi Izraelci ostaviše Davida i pođoše za Bikrijevim sinom Šebom; a Judejci prionuše uza svoga kralja i otpratiše ga od Jordana do Jeruzalema.
Saboda haka dukan mutane Isra’ila suka bar Dawuda don su bi Sheba ɗan Bikri. Amma mutanen Yahuda suka kasance a wurin sarki tun daga Urdun har zuwa Urushalima.
3 Kad se David vratio u svoju palaču u Jeruzalem, uze deset inoča koje je bio ostavio da čuvaju palaču i stavi ih da budu čuvane. Brinuo im se za uzdržavanje, ali nije više išao k njima. Tako su one živjele zatvorene do svoje smrti, kao udovice živoga muža.
Da Dawuda ya komo fadarsa a Urushalima, sai ya ɗauko ƙwarƙwaran goma nan da ya bari su lura da fada, ya keɓe su a wani gida inda za a yi tsaronsu. Ya tanada musu, amma bai kwana da su ba. Aka sa su a keɓe har iyakar rayuwarsu, suka yi zama kamar gwauraye.
4 Potom kralj zapovjedi Amasi: “Sazovi mi Judejce do tri dana, a i ti da budeš ovdje!”
Sa’an nan sarki ya ce wa Amasa, “Ka tattaro mutanen Yahuda su zo wurina cikin kwana uku, kai kuwa ka kasance a can kai kanka.”
5 Amasa ode da sazove Judejce, ali se zadrža preko vremena koje mu bijaše odredio kralj.
Amma da Amasa ya tafi kiran mutanen Yahuda, ya ɗauki lokaci fiye da lokacin da sarki ya ba shi.
6 Tada David reče Abišaju: “Sad će nam Bikrijev sin Šeba biti opasniji nego Abšalom. Zato uzmi ljude svoga gospodara i pođi za njim u potjeru da se ne domogne tvrdih gradova i ne izmakne nam iz očiju!”
Dawuda ya ce wa Abishai, “Ina gani Sheba ɗan Bikri zai ba mu wuya fiye da Absalom. Ka ɗauki mutanen maigidanka ka fafare shi, don kada yă sami garuruwa masu katanga yă tsere mana.”
7 Za Abišajem krenu na put Joab, Kerećani, Pelećani i svi junaci; oni iziđu iz Jeruzalema u potjeru za Bikrijevim sinom Šebom.
Saboda haka mutanen Yowab da Keretawa da Feletiyawa da dukan jarumawa suka fita a ƙarƙashin Abishai. Suka fita daga Urushalima don su fafari Sheba ɗan Bikri.
8 Kad su bili kod velikoga kamena što je kod Gibeona, dođe Amasa prema njima. Joab imaše na sebi ratnu haljinu, a preko nje imaše pripasan mač uz bedro, u koricama; ali mu se mač iskliznu i pade.
Yayinda suke a babban dutse a Gibeyon, Amasa ya zo don yă tarye su. Yowab kuwa yana sanye da doguwar rigar soja, a ɗamarar da ya sha kuwa akwai wuƙa a cikin kube. Da ya zo gaba sai wuƙar ta zāre daga kube ta fāɗi.
9 Joab pozdravi Amasu: “Jesi li mi dobro, brate?” I desnom rukom uhvati za bradu Amasu da ga poljubi.
Yowab ya ce wa Amasa, “Yaya kake, ɗan’uwana?” Sai Yowab ya kama gemun Amasa da hannun dama don yă yi masa sumba.
10 Amasa se nije obazirao na mač koji bijaše Joabu u ruci, i on ga udari njim u trbuh i prosu mu utrobu na zemlju. Nije morao ponoviti udarac i Amasa umrije. Joab sa svojim bratom Abišajem nastavi potjeru za Bikrijevim sinom Šebom.
Amasa kuwa bai lura da wuƙar da take hannun Yowab ba, Yowab kuwa ya soke shi da wuƙar a ciki, hanjinsa suka zube ƙasa. Ba tare da ƙarin suƙa ba, Amasa ya mutu. Sa’an nan Yowab da ɗan’uwansa Abishai suka fafari Sheba ɗan Bikri.
11 Jedan od Joabovih momaka osta na straži kod Amase i tu je vikao: “Kome je mio Joab i tko je za Davida neka slijedi Joaba!”
Ɗaya daga cikin mutanen Yowab ya tsaya kusa da Amasa ya ce, “Duk mai son Yowab, kuma duk mai son Dawuda, yă bi Yowab!”
12 A Amasa ležao u krvi nasred puta. Videći onaj čovjek gdje se ustavlja sav narod, odvuče Amasu s puta u polje i baci preko njega kabanicu jer je vidio gdje se zaustavlja svatko tko naiđe blizu njega.
Amasa kuwa yana kwance cikin tafkin jininsa a kan hanya, sai mutumin ya ga dukan sojoji suka zo suka tsaya cik a can. Da ya gane cewa duk wanda ya haura zuwa wurin Amasa sai ya tsaya, sai ya ja gawar Amasa daga hanyar ya kai can cikin wani fili ya rufe shi da zane.
13 Kad je Amasa bio uklonjen s puta, svi ljudi pođoše za Joabom da gone Bikrijeva sina Šebu.
Bayan an ɗauke Amasa daga hanya, sai dukan mutane suka bi Yowab don fafaran Sheba ɗan Bikri.
14 Šeba je prošao kroza sva izraelska plemena sve do Abel Bet Maake i svi Bikrani s njim. Skupiše se oni i pođoše za njim.
Sheba ya bi ta dukan kabilan Isra’ila zuwa Abel da kuma ta dukan yankin Beriyawa, waɗanda suka taru suka bi shi.
15 Joab dođe i opsjede ga u Abel Bet Maaki. Dade nasuti nasip oko grada. Sva vojska koja bijaše s Joabom navali potkopavati zid da ga obori.
Sai dukan rundunonin da suke tare da Yowab suka zo suka yi wa Sheba kwanton ɓauna a Abel-Bet-Ma’aka. Suka tara ƙasa kewaye da jikin katangar birnin daidai da tsayinta. Sa’an nan waɗansu kuma suna ƙoƙarin rushe katangar.
16 Tada se jedna mudra žena uspe na zid i povika iz grada: “Čujte! Čujte! Recite Joabu: 'Priđi ovamo, da govorim s tobom!'”
Sai wata mata mai hikima ta yi kira daga ciki birnin ta ce, “Ku saurara! Ku saurara! Ku gaya wa Yowab yă zo nan ina so in yi magana da shi.”
17 Kad je prišao, upita žena: “Jesi li ti Joab?” On odgovori: “Jesam.” A ona će: “Poslušaj riječ sluškinje svoje!” On odgovori: “Slušam.”
Ya tafi wurinta, sai ta ce, “Kai ne Yowab?” Ya ce, “Ni ne”. Ta ce, “Ka ji abin da zan ce maka.” Ya ce, “Ina jinki.”
18 Žena nastavi: “Nekoć se govorilo ovako: 'Treba pitati u Abelu i u Danu
Ta ci gaba ta ce, “A dā can, akan ce, ‘Sami amsarka a Abel,’ shi ke nan an gama.
19 je li svršeno s onim što su utvrdili vjernici u Izraelu.' Ti bi htio uništiti jedan grad, i to jedan od matičnih gradova u Izraelu. Zašto zatireš baštinu Jahvinu?”
Mu ne masu salama da kuma amintattu na Isra’ila. Kana ƙoƙari ka hallaka birnin da yake uwa a Isra’ila. Don me kake so ka hallakar da gādon Ubangiji?”
20 Joab odgovori ovako: “Daleko, daleko bilo to od mene! Ne želim ni zatirati ni razarati.
Yowab ya ce, “Allah yă sawwaƙe! Allah yă sawwaƙe in hallaka, ko in lalace gādon Ubangiji.
21 Ne radi se o tome, nego je jedan čovjek iz Efrajimove gore, po imenu Šeba, Bikrijev sin, podigao ruku na kralja, na Davida. Predajte samo njega, pa ću otići od grada!” Žena odgovori Joabu: “Dobro. Odmah će ti njegovu glavu baciti preko zida!”
Ba haka ba ne batun. Wani mai suna Sheba ɗan Bikri ne, daga ƙasar tudun Efraim, ya tayar wa sarki, yana gāba da Dawuda. Ki ba mu wannan mutum, zan kuwa janye daga birnin.” Matar ta ce wa Yowab, “Za a jefa maka kansa daga katanga.”
22 Žena se vrati u grad i progovori svemu narodu kako joj je govorila njezina mudrost. I odsjekoše glavu Bikrijevu sinu Šebi i baciše je Joabu. A on zapovjedi da zatrube u rog te se raziđoše od grada, svaki u svoj kraj. A Joab se vrati kralju u Jeruzalem.
Sa’an nan matar ta tafi wurin dukan mutane da shawararta mai hikima, sai suka datse kan Sheba ɗan Bikri suka jefa wa Yowab. Saboda haka sai ya busa ƙaho, mutanensa kuwa suka watse daga birnin, kowa ya koma gidansa. Yowab kuma ya koma wurin sarki a Urushalima.
23 Joab je bio zapovjednik nad svom vojskom. Jojadin sin Benaja bio je zapovjednik nad Kerećanima i Pelećanima.
Yowab ne yake shugabancin dukan rundunoni; Benahiya ɗan Yehohiyada ne yake shugabancin Keretawa da Feletiyawa;
24 Adoram je bio nadglednik nad radovima. Ahiludov sin Jošafat bio je pečatnik.
Adoniram kuwa shi ne shugaban aikin gandu; Yehoshafat ɗan Ahilud shi ne marubucin tarihi;
25 Seraja je bio državni pisar. Sadok i Ebjatar bijahu svećenici.
Shewa kuwa magatakarda; Zadok da Abiyatar su ne firistoci;
26 Uz to je Jairanin Ira bio zamjenik Davidov.
Ira mutumin Yayir kuwa shi ne firist na Dawuda.