< 2 Ljetopisa 7 >
1 Kad Salomon dovrši molitvu, spusti se oganj s neba i spali paljenicu i klanice i slava Jahvina ispuni Dom.
Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
2 Svećenici ne mogoše ući, jer slava Jahvina bješe ispunila Dom Jahvin.
Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
3 Svi sinovi Izraelovi, videći gdje se oganj sa slavom Jahvinom spustio na Dom, padoše ničice k zemlji do kamenog poda; pokloniv se, počeše slaviti Jahvu “jer je dobar i jer je vječna njegova ljubav”.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
4 Potom kralj i čitav narod stadoše žrtvovati žrtve pred Jahvom.
Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
5 Kralj Salomon prinese za žrtvu dvadeset i dvije tisuće goveda, sto i dvadeset tisuća ovaca; i tako posvetiše Dom Jahvin i kralj i sav narod.
Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
6 Dok su svećenici stajali na dužnostima, leviti su na glazbalima za Jahvine pjesme, što ih učini kralj David, slavili Jahvu “jer je vječna njegova ljubav”. Time je David preko njihovih ruku hvalio Jahvu. Pred njima su svećenici trubili u trube, dok su Izraelci stajali.
Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
7 Salomon je posvetio i sredinu predvorja koje je pred Jahvinim Domom, jer je ondje prinio paljenice i pretilinu od pričesnica, jer na tučani žrtvenik koji bijaše napravio Salomon nisu mogle stati paljenice ni prinosi ni pretilina.
Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
8 U to je doba Salomon svetkovao blagdan sedam dana i sav Izrael s njime, vrlo velik zbor, od Ulaza u Hamat pa do Egipatskoga potoka.
Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
9 A osmoga su dana svetkovali svečani zbor, jer su posvetu žrtveniku svetkovali sedam dana i blagdan sedam dana.
A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
10 Dvadeset trećega dana sedmoga mjeseca posla ljude k njihovim šatorima i odoše vesela i zadovoljna srca zbog dobra koje je Jahve učinio Davidu i Salomonu i svem narodu izraelskom.
A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
11 Tako je Salomon dovršio Dom Jahvin i kraljevski dvor i izveo sve što god bješe zasnovano da izvrši u Domu Jahvinu i u svojem dvoru.
Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
12 Potom se Jahve ukaza Salomonu noću i reče mu: “Uslišao sam tvoju molitvu i izabrao to mjesto da mi bude Dom žrtve.
sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
13 Ako zatvorim nebo da ne bude dažda, ili zapovjedim skakavcima da popasu zemlju, ili pustim kugu na svoj narod,
“Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
14 i ponizi se moj narod na koji je prizvano Ime moje i pomoli se i potraži lice moje i okani se zlih putova, ja ću ga tada uslišati s neba i oprostiti mu grijeh i izliječit ću mu zemlju.
in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
15 Moje će oči biti otvorene i moje uši pažljive na molitvu s ovoga mjesta.
Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
16 Sada sam, dakle, izabrao i posvetio ovaj Dom da ovdje bude Ime moje zauvijek i ovdje će sve dane biti moje oči i moje srce.
Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
17 A ti, budeš li išao preda mnom kako ti je išao otac David, vršeći sve što sam ti zapovjedio i držeći se mojih uredaba i zakona,
“Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
18 uzdržat ću tvoje kraljevsko prijestolje kako sam obećao tvome ocu Davidu govoreći: 'Neće ti ponestati nasljednika koji bi vladao u Izraelu.'
zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
19 Ali ako me ostavite i napustite uredbe i zapovijedi koje sam vam dao te otiđete i počnete služiti tuđim bogovima i klanjati im se,
“Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
20 istjerat ću Izraelce iz svoje zemlje koju sam im dao i odbacit ću od sebe ovaj Dom koji sam posvetio svojem Imenu i učinit ću od njega priču i sramotu među svim narodima.
zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
21 Tko god prođe mimo ovaj Dom koji bijaše preslavan zaprepastit će se od užasa i pitati: 'Zašto je Jahve tako učinio s ovom zemljom i s ovim Domom?'
Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
22 I odgovorit će mu se: 'Ostavili su Jahvu, Boga svojih otaca, koji ih je izveo iz Egipta, i okrenuli se tuđinskim bogovima, i klanjali im se, i služili im, i zato je Jahve pustio na njih sve ovo zlo.'”
Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”